An haifi yaro namiji, a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya, wanda ya zo da gangar jiki daya, da kai biyu, idanu hudu, baki biyu da kuma hanci biyu.
Hukumar alhazan Najeriya (NAHCON) ta ayyana farashin kujerar hajjin bana da ya doshi Naira miliyan 5.
An kama Badejo ne bayan ya kafa wata kungiyar 'yan sa-kai ta Fulani zalla, domin taimakawa wajen inganta tsaron mambobinta a jihar Nasarawa da ma wasu wurare da ake fama da matsalar tsaro.
Wasu daga cikin jihohin da aka yi zaben sun hada da Filato, Nasarawa, Kaduna, Binuwe, Ebonyi, Yobe, Ondo, Taraba, Borno, Kebbi da Legas.
Najeriya ta doke Angola ci 1-o a wasar Kwatal final na gasar AFCON da aka fafata a filin wasa na Félix Houphouët Biogny da ke Abidjan.
Wasu mutane dauke da makamai sun harbe wani basaraken gargajiya, tare da yin garkuwa da matarsa da kuma wani mutum guda a yankin arewa maso tsakiyan Najeriya, kamar yadda hukumomi suka bayyana.
Gamayyar kungiyoyin fararen hula sama da 40 sun kai karar Shugaban Najeriya Bola Tinubu, inda suka yi kira gare shi da ya magance matsalar rashin tsaro da ta kara kamari tun bayan hawansa mulki a watan Mayun da ya gabata.
Amurka ta sake nanata kudurinta na tsayawa tsayin daka a fannin tattalin arziki da kasuwanci a kasashen Afirka.
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, ta cire jami'iyyar PDP a jerin jami'iyyun da zasu shiga zaben da zata gudanar na 'yan majalisun tarayya a shiyyar Arewacin jahar Filato.
Bayan shafe dare da wuni daya su na yajin canjin kudi, 'yan kasuwar canji a Abuja sun tsaida shawarar janye yajin don komawa aiki a yau jumma'a.
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya kalubalanci hukumar EFCC, mai yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya, data kara kaimi a yakin da take yi da annobar damfara ta hanyar amfani da kafar sadarwa ta intanet da sauran nau'ukan almundahana.
Daraktan Cibiyar Samar da Bayanai a Hedkwatar Rundunar Tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba ya ce suna sane da kalubalen tsaron da a halin yanzu ake fuskanta a sassa daban-daban na kasar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.