Tsohon shugaban Najeriya kuma daya daga cikin wadanda suka kafa kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin nahiyar Afrika, Janar Yakubu Gowon, ya bukaci ECOWAS ta dage takunkumin da ta kakabawa kasashen Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar.
Shugaba Bola Tinubu ya nada Kemi Nanna Nandap a matsayin sabuwar Shugabar Hukumar Shige da fice ta Kasar Najeria.
Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) tayi kira ga kungiyar kwadago ta NLC, da ta jingine shirinta na gudanar da zanga-zanga domin ci gaba da wanzuwar zaman lafiya da walwalar jama’a.
Hadaddiyar Kungiyar Kwadago ta Najeriya ta tsunduma cikin wani yajin aikin sai baba ta gani a jihar Neja, inda ta rufe ofisoshin gwamnati da asibitoci.
Kamfanonin simintin Najeriya sun amince su rage farashinsa zuwa tsakanin naira dubu 7 da dubu 8 akan buhu mai nauyin kilogiram 50 y danganta akan nisan wurin a fadin kasar.
Masana tattalin arziki sun ce ba 'yan canjin kasuwannin bayan fagge ke yi wa tattalin arzikin Najeriya gagarumar illa ba, wasu shugabannin bankunan kasuwancin kasar ne.
Babban hafsan tsaron Najeriya ya bayyana takaicinsa a yau Talata kan abin da ya kira rashin adalcin wasu kasashen da ke kin sayar da makaman soji wa Najeriya ta wajen rabewa da bukatar kare hakkin bil'adama.
Sanarwar Bankin na kunshe ne a cikin wani rahoto da aka fidda a makon jiya.
A kokarinta na saukakawa matafiya zirga-zirga a filayen tashi da saukar jiragen kasar, gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na kaddamar da kofofi masu amfani da na’urar lantarki a filin saukar jiragen saman kasa da kasa a Najeriya a watan Maris me kamawa.
Kungiyar ta janye yajin aikin da ta fara a jiya Litinin bayan shiga tsakani da gwamnatin tarayya ta yi tsakaninta da sauran masu ruwa da tsaki a fannin albarkatun man fetur kamar NNPCL, NMDPRA, DAPPMA da dai sauran su
Hukumar Kididdiga ta Najeriya, NBS, ta bayyana cewar, an samu gagarumar karuwa a mizanin rashin aikin yi a Najeriya a zango na 3 na shekarar 2023.
Kotun Shari'ar Musulunci da ke zamanta a Kano ta bukaci da a duba lafiyar kwakwalwar shahararriyar yar Tiktok, Murja Ibrahim Kunya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.