Wata gobara da ta tashi ta lalata shaguna da dama a babbar kasuwar Gusau, na jihar Zamfara a Najeriya, inda ta kashe mutum daya.
Kotun Koli ta tabbatar da nasarar Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan jihar Adamawa inda mai shari’a John Okoro wanda ya shirya kuma ya karanta hukuncin a ranar Laraba ya yi watsi da karar da ‘yar takarar gwamna a karkashin inuwar jam’iyyar APC, Aisha Dahiru ta shigar.
Najeriya ta yi Allah Wadai da ficewar Jumhuriyar Nijar, Mali da Burkina Faso daga Kungiyar ECOWAS ko CEDEAO duk da cewa ya zuwa yau Kungiyar ta ce ba ta samu wata sanarwar ficewar kasashen ba.
A ranar Litinin da daddare ne wasu ‘yan bindiga a Najeriya suka yi garkuwa da dalibai shida da malamai uku daga wata makaranta da ke kudu maso yammacin jihar Ekiti, kamar yadda gwamnatin jihar ta bayyana a ranar Talata, a wani rahoton na sace yara ‘yan makaranta da aka yi a kasar na farko bana.
Najeriya ta ce hukumomin sojin kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso wadanda ba zababbun al’umman kasar ba ne sun zalunci al’ummarsu yayin da su ka dauki matakin hadin gwiwa na ficewa daga kungiyar ECOWAS.
Wasu da ake zargin mayakan IS ne sun kashe mutane 22 a hari da suka kai a wani kauye da ke yammacin Jamhuriyar Nijar kusa da kan iyaka da Mali, kamar yadda wasu majiyoyi na cikin gida suka shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa a ranar Litinin.
Kotun Koli ta jingine hukunci a karar da jam’iyyar APC da ‘yar takar gwamna a zaben da aka gudanar a ranr 18 ga Maris din 2023, Aisha Binani, wacce aka fi sani da Binani su ka shigar akan gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri.
Ademola Lookman mai buga wa kungiyar kwallon kafa ta Atalanta a kasar Italiya ne ya zura wa Najeriya kwallaye biyu.
Masu garkuwa da mutane sun bukaci a biya Naira miliyan 200 kudin fansa domin sako shugaban PDP na Legas da suka sace.
Wani jirgin mai lamba N580KR , dauke ne da wasu muhimman mutane da kawo yanzu ba a bayyana sunayesu ba, ya yi hadari a Ibadan, babban birnin jihar Oyo a kudu maso yammacin Najeriya.
A wani mataki da kotun kolin Najeriya ta yanke, ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar da aka yankewa tsohon dan majalisar wakilai Farouk Lawan, bisa samunsa da laifin cin hanci da rashawa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.