Kungiyar kwallon kafa ta Chippa United ta wallafa a shafinta na X cewar, Nwabali na daga cikin ‘yan wasan da suka yi fice a gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON) na shekarar 2023.
Tashar talabijin ta Channels ta ruwaito cewar, dalibai 20 sun mutu a wasu makarantun sakandaren kwana na ‘yan mata guda 3 da kuma Kwalejojin Gwamnatin Tarayya na ‘yan mata dake kananan hukumomin Potiskum da Fika a jihar Yobe sakamakon barkewar cutar da ake zargin sankarau ce.
A yau talata, mambobin kungiyar kwadago ta NLC suka kutsa kai cikin ginin Majalisar Tarayyar Najeriya dake Abuja a ci gaba da zanga-zangar da suke yi game tsadar rayuwa a kasar.
Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da nadin Hafsat Bakari a matsayin darakta a hukumar kula da hada-hadar kudi ta Najeriya wato NFIU.
Kwamitin tsare-tsaren tsaren manufofin kudin babban Bankin Najeriya wato MPC na CBN ya kara kudin ruwa da maki dari hudu daga kaso 18 da digo 75 zuwa kaso 22 da digo 75.
Mambobin Kungiyar Kwadago ta Najeriya wato NLC sun gudanar da zanga-zanga a fadin kasar sakamakon matsin rayuwa, yunwa da tabarbarewar tattalin arziki a kasar.
Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Olayemi Cardoso, yace bai kamata a kyale harkar canjin kudade ta zama “ta ci barkatai” ba, inda yace bankin na kokarin fitar da wasu tsauraran ka’idoji domin tsaftace harkar da nufin kawar da ‘yan kayi nayi daga cikinta.
Majalisar Zartarwa ta Tarayya ta amince da aiwatar da wani sashe na rahoton kwamitin Stephen Orasanye kan hada wasu hukumomin da ma'aikatun gwamnati a wuri guda, a yayin da wasu kuma za'a sauya musu fasali ko kuma a rushesu sannan wasu kuma a sauya musu matsugunai.
Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta tsayar da ranakun 19 da 20 ga watan Maris mai kamawa domin ci gaba da sauraron shari'ar jagoran haramtacciyar kungiyar 'yan awaren Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu dake fuskantar tuhuma akan zargin cin amanar kasa.
Wani Sojin Saman Amurka ya mutu bayan da ya cinnawa kansa wuta a wajen ofishin jakadancin Isra'ila da ke Washington, D.C., yayin da ya bayyana cewa “ba zai kara kasancewa ba cikin masu kisan kare dangi.”
Matsin tattalin arziki a fadin Najeriya ya harzuka ‘yan kasa inda suka bazama kan tituna a wasu jihohi don nuna rashin jin dadinsu dangane da tashin gwauron zabin kayayyakin abinci da tsadar rayuwa a kasar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.