A watan Fabrairun da mu ke ciki ne ake sa ran za a fara tonon albarkatun man fetur da iskar gas da aka samu a Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe.
A yau litinn, mazauna Minna, babban birnin jihar Neja sun gudanar da zanga-zanga game da tsadar rayuwa a Najeriya, inda suka toshe manyan titunan birnin.
Yayin da mahukunta ke kan daukar matakan dakile ayukkan 'yan bindiga a wasu sassa na Najeriya, su kuwa 'yan bindigar na kara kai farmaki ga al'ummomi musamman wadanda ke zaune a wurraren da ke fama da rashin tsaro.
Tsohon gwamnan jihar Yobe Sanata Bukar Abba Ibrahim ya rasu yana da mai shekaru 75.
Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya ta dakatar da wani jami'inta mai suna Mr Fred Ogboji, wanda ke kula da karamar hukumar Jos ta Arewa, bisa zargin bacewar wasu muhimman kayayyakin gudanar da zabe.
An haifi yaro namiji, a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya, wanda ya zo da gangar jiki daya, da kai biyu, idanu hudu, baki biyu da kuma hanci biyu.
Hukumar alhazan Najeriya (NAHCON) ta ayyana farashin kujerar hajjin bana da ya doshi Naira miliyan 5.
An kama Badejo ne bayan ya kafa wata kungiyar 'yan sa-kai ta Fulani zalla, domin taimakawa wajen inganta tsaron mambobinta a jihar Nasarawa da ma wasu wurare da ake fama da matsalar tsaro.
Wasu daga cikin jihohin da aka yi zaben sun hada da Filato, Nasarawa, Kaduna, Binuwe, Ebonyi, Yobe, Ondo, Taraba, Borno, Kebbi da Legas.
Najeriya ta doke Angola ci 1-o a wasar Kwatal final na gasar AFCON da aka fafata a filin wasa na Félix Houphouët Biogny da ke Abidjan.
Wasu mutane dauke da makamai sun harbe wani basaraken gargajiya, tare da yin garkuwa da matarsa da kuma wani mutum guda a yankin arewa maso tsakiyan Najeriya, kamar yadda hukumomi suka bayyana.
Gamayyar kungiyoyin fararen hula sama da 40 sun kai karar Shugaban Najeriya Bola Tinubu, inda suka yi kira gare shi da ya magance matsalar rashin tsaro da ta kara kamari tun bayan hawansa mulki a watan Mayun da ya gabata.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.