Farashin hannun jari Access Holdings na Najeriya ya fadi da kaso 6.26 a yau yayin da masu hannun jari a kamfanin ke alhinin rasuwar Herbert Wigwe.
Al’umomin garuruwan yammacin Zaria sun koka kan hauhawar hare-haren 'yan-bindiga a yankin da su ka ce kullum sai an kashe musu mutane kuma a sace wasu don karbar kudin fansa.
Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya wato NDLEA sun kama wani mutum mai shekaru 42 da aka ce yana jigilar dubunnan miyagun kwayoyin na Opiod a boye zuwa wani yanki na ‘yan tada kayar baya a yankin Banki na jihar Borno.
Ministar kasuwanci ta Burtaniya, Kemi Badenoch ta isa Najeriya domin fara ziyarar aiki ta kwanaki uku, da nufin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Burtaniya da Najeriya.
Masaukin Bakin gasar kofin nahiyar Afirka ta bana, Ivory Coast, ta lashe gasar bayan ta ci Najeriya 2-1 a wasan karshe na AFCON
Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba.
Zuwa yanzu hukumomi a Amurka da Najeriya, da kuma wasu masu fada a ji a Najeriya, sun tabbatar da mutuwar babban shugaban Bankin Access da iyalinsa.
Da alamar gwamnatin Najeriya ta fara daukar matakin rage matsalar rashin abinci da tsadarsa a fadin kasar biyo bayan korafe korafe da zanga zangar da aka yi a wasu sassan kasar kan tsadar rayuwa.
Tsadar rayuwa da hauhawar kayan masarufi, wani abu ne da ya addabi ƴan Najeriya, wanda kuma a tarihin kasar, ba'a taba fuskantar irin wannan kunci na rayuwa ba, wanda har yasa wasu gudanar da zanga-zanga.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.