Fitattaciyar ‘yar TikTok Murja Ibrahim Kunya ta shigar da kara gaban babbar kotun jihar Kano, bisa zargin keta mata haddi da rashin bin ka’idojin da kundin tsarin mulkin Najeriya ya bayar wajen shigar da karar da ake tuhumarta.
Babban Bankin Najeriya CBN ya soke lasisin wasu kamfanonin canjin kudi 4,173, cikin kimanin 5000 da ake da su.
Ba za a sami nasarar hade layikan salula da lambar Shaidar Dan Kasa ba idan ana amfani da karfin iko a maimakon bin mutane da lalama a cewar masana.
Kamen masu aikata badala a wasu sassa na birni da kewayen Kano da damkewa tare da gurfanar da matashiyar nan da ke kalaman batsa Murja Kunya a kotu, na daga cikin abubuwan da suka sabbaba wannan takaddama.
Kasa da kwana 2 da rufe layikan sadarwa al’ummar Najeriya na kokawa a kan yadda wannan matakin ke ci gaba da jawo musu asara kuma wasu masana ke cewa a cikin lallami ya kamata a bi yan kasa don hade layukansu da lambar shedar dan kasa, wasu kuma na ganin dole a Fifita ‘yancin ‘yan kasa a kan komai.
A ranar 1 ga watan Maris din shekarar 2024, Babban Kwamandan Hisbah, Sheikh Daurawa ya yi murabus daga mukaminsa kan kalaman na gwamna Abba Kabir Yusuf wadanda suka soki ayyukan da Hisbah ke yi.
Jose Peserio ya sanar da gama aikinsa na horar da 'yan wasan tawagar Super Eagles ta Najeriya bayan tawagar ta kai wasan karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta AFCON a kasar Ivory Coast.
A safiyar yau Juma’a 1 ga watan Maris ne kwamandan Hisbah Sheikh Aminu Daurawa ya bayyana ajiye aikinsa na shugaban hukumar a shafinsa na Facebook biyo bayan rashin samun goyon baya wajen gudanar da ayyukan kauda badala.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah wadai da zanga-zangar da kungiyar Najeriya NLC ta yi a fadin kasar domin nuna adawa da tsadar rayuwa da yunwa, inda ya gargadi kungiyar kwadago da ta sani cewa, ba ita kadai ce muryar jama’a ba.
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya kaddamar da layin dogo 'Red line' na zamani a birnin Legas.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.