Majalisar Zartarwa ta Tarayya ta amince da aiwatar da wani sashe na rahoton kwamitin Stephen Orasanye kan hada wasu hukumomin da ma'aikatun gwamnati a wuri guda, a yayin da wasu kuma za'a sauya musu fasali ko kuma a rushesu sannan wasu kuma a sauya musu matsugunai.
Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta tsayar da ranakun 19 da 20 ga watan Maris mai kamawa domin ci gaba da sauraron shari'ar jagoran haramtacciyar kungiyar 'yan awaren Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu dake fuskantar tuhuma akan zargin cin amanar kasa.
Wani Sojin Saman Amurka ya mutu bayan da ya cinnawa kansa wuta a wajen ofishin jakadancin Isra'ila da ke Washington, D.C., yayin da ya bayyana cewa “ba zai kara kasancewa ba cikin masu kisan kare dangi.”
Matsin tattalin arziki a fadin Najeriya ya harzuka ‘yan kasa inda suka bazama kan tituna a wasu jihohi don nuna rashin jin dadinsu dangane da tashin gwauron zabin kayayyakin abinci da tsadar rayuwa a kasar.
Shelkwatar tsaro ta Najeriya ta musanta zargin faruwar wasu al’amura da ba’a saba gani ba da ya sabbaba zargin yunkurin juyin mulki a kasar da wata kafar yada labarai ta intanet ta yada ta na mai cewa hakan ya yi sanadin "sanya dakarun tsaron adar Shugaban Kasa cikin shirin ko-ta-kwana.
A ltitinin din nan, mambobin kungiyoyin fafutukar farar hula sun fantsama kan titunan jihohin Edo da Osun akan halin matsin rayuwar da ake fama da shi a Najeriya.
Najeriya ta amince da dawo da hasken wutar lantarki ga jamhuriyar Nijar bayan janye wasu takunkumai da Kungiyar Raya Tattalin Arziki Kasashen Afrika ta Yamma, ECOWAS, ta yi kan kasar.
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirta ta Yamma, ECOWAS, ta amince da ta dage wasu takunkumai da ta kakabawa kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso da kuma Guinea.
Yayin da talakan Najeriya ke ci gaba da dandana kudarsa, hankula na dada karkata kan rawar da tashin farashin dala ke takawa.
Akeredolu ya rasu a kasar Jamus a ranar 27 ga watan Disambar bara bayan fama da rashin lafiya. Shekarunsa 67.
A cewar masanin, lokaci ya yi da matasa za su kara mayar da hankalinsu kan koyon ilimin na'ura mai kwakwalwa wanda hakan zai ba su dama su yi aiki daga ko'ina a duniya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.