A kokarinta na saukakawa matafiya zirga-zirga a filayen tashi da saukar jiragen kasar, gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na kaddamar da kofofi masu amfani da na’urar lantarki a filin saukar jiragen saman kasa da kasa a Najeriya a watan Maris me kamawa.
Kungiyar ta janye yajin aikin da ta fara a jiya Litinin bayan shiga tsakani da gwamnatin tarayya ta yi tsakaninta da sauran masu ruwa da tsaki a fannin albarkatun man fetur kamar NNPCL, NMDPRA, DAPPMA da dai sauran su
Hukumar Kididdiga ta Najeriya, NBS, ta bayyana cewar, an samu gagarumar karuwa a mizanin rashin aikin yi a Najeriya a zango na 3 na shekarar 2023.
Kotun Shari'ar Musulunci da ke zamanta a Kano ta bukaci da a duba lafiyar kwakwalwar shahararriyar yar Tiktok, Murja Ibrahim Kunya.
Kudirin neman yiwa kundin tsarin mulkin Najeriya kwaskwarima domin kirkirar ‘yan sandan jihohi ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar wakilan kasar.
Wasu gungun ‘yan bindiga sun kai hari a ofishin ‘yan sanda a garin Zurmi da ke jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya, amma jami’ansu sun fatattaki su yayin da aka samu asarar rayuka a bangarorin biyu, in ji rundunar ‘yan sandan a ranar Litinin.
Shugaban hukumar yaki da cin hanci ta ICPC, Dakta Musa Adamu Aliyu ya ce ba lalle sai an kafa kotuna na musamman ba don sauraron shari'un cin hanci da rashawa.
Bayan samun labarin ba wa Murjah Ibrahim Kunya beli, kafafen sadarwa ya cika da jita-jitar cewar Kwamandan Hisbah, Shiek Aminu Ibrahim Daurawa, ya ajiye aikinsa sakamakon ba da belin da kotu ta yi.
Shugabanni a gundumar Kufanan karamar hukumar Kajurun da 'yan bindiga su ka kai hari, sun ce kone mutane da rumbunan abinci da aka yi babbar barazana ce ga al-umar garin Gindin Dutse Makyalin.
Shugaban Ghana, Nana Akufo-Addo, ya yi kira ga shugabanni da gwamnatocin kasashen Afirka da su hada kai, su dau matakin zuba hannun jari na kashi talatin cikin dari a cibiyoyin hada-hadar kudi na Afirka da nufin inganta ma’aunin wadannan cibiyoyi yadda za su tallafawa ci gaban Afirka.
‘Yan Najeriya na fuskantar daya daga cikin yanayi mafi muni na tabarbarewar tattalin arziki a kasar ta Yammacin Afirka a cikin shekaru da dama sakamakon hauhawar farashin kayayyaki.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.