‘Yan Najeriya na fuskantar daya daga cikin yanayi mafi muni na tabarbarewar tattalin arziki a kasar ta Yammacin Afirka a cikin shekaru da dama sakamakon hauhawar farashin kayayyaki.
NLC ta ce za ta shiga yajin aikin a ranakun 27 da 28 na wannan wata na Fabrairu don jan hankalin hukumomi kan yadda ‘yan Najeriya ke fama da matsin rayuwa.
Hukumar kare hakkin masu sayan kaya ta kasa (FCCPC), ta rufe katafaren kantin Sahad Store, a unguwar Garki dake birnin Abuja.
Farashin kaya a Najeriya na cigaba da tashi babu kakkautawa a farkon shekara nan, kamar yadda hukumar kididdiga ta kasa NBS ta bayyana a rahoton da ta fitar.
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya umarci Mai Bashi Shawara Akan Harkokin Tsaro, Nuhu Ridadu da babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetokun da Darakta Janar Na Hukumar Tsaron Farin Kaya Ta Dss, Yusuf Bichi su hada kai da gwamnonin jihohi wajen farautar ‘yan kasuwar dake boye kayan abinci.
Gwamnatocin tarayya da na jihohin Najeriya 36 na nazari akan bukatar kafa rundunonin ‘yan sandan jihohi.
A yayın da ‘yan Najeriya ke ci gaba da kokawa kan tsananin rayuwa sakamakon tsadar abinci, magunguna da wasu ababen rayuwar yau da kullum, gwamnatin Najeriya ta bakın Ministan Noma, ta ce nan da mako mai zuwa, zata fara raba hatsi kyauta ga manoma musamman mabukata don rage matsalar yunwa a kasar.
Hukumar kula da hakar albarkatun man ta Najeriya (NUPRC) na duba yiyuwar mayar da wasu daga cikin ofisoshinta daga Abuja zuwa Legas, a cewar wata sanarwar da Dr. Kelechi Onyekachi Ofoegbu ya fitar a madadinta.
Kungiyar GTA a majalisar wkilai su 60 ta fara wannan yunkurin ne tare da neman a koma tsarin Majalisa da aka yi amfani da a jamhuriya ta farko a Najeriya, saidai wani kwararre da ma wata fitacciyar ‘yar siyasa a Najeriya sun bayyana ra'ayoyi mabanbanta kan wanna yunkurin.
A kokarin da suke yi na ganin sun samar da tsaro a yankunan jihar Filato da ke fama da tashe-tashen hankula, rundunar sojojin Operation SAFE HAVEN da hadin gwiwan rundunar Operation HAKORIN DAMISA IV sun samu tarwatsa wani wurin kera makamai.
Masu kamfanonin buredi a Najeriya sun ce suna daf da rufe kamfanoninsu saboda matsalar tashin gwauron zabi da kayan sarrafa buredin ke yi a halin yanzu.
Gwamnatin tarayyar Najeriya na neman ma’aikacin CBN, Odoh Ocheme da wasu mutane biyu bisa zargin sa hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari na jabu na satar kudi $6.2m daga babban bankin kasar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.