Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sace wasu daliban makarantar allo ta almajirao a wani kauye da ake kira Gidan Bakuso a jihar Sokoto da ke Najeriya.
Asusun Tallafawa Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) yayi Allawadai da harin baya-bayan nan da aka kai kan wata makaranta a jihar kaduna.
Shugaban Kasar Najeriya, Bola Tinubu, ya sha alwashin cewar gwamnatinsa zata bada fifiko kan walwalar mata da kiyaye hakkokinsu tare da bunkasa rayuwarsu.
A yayın da ake bukin Ranar Mata ta Duniya a yau Juma’a 8 ga watan Maris na shekarar 2024, wanda aka yiwa taken Zuba jari ga mata: Habaka ci gaba, dubban mata na jan hankali a kan yiyuwar jefa Mata miliyan 340 a duniya cikin tsananin talauci idan ba’a dauki matakan da suka dace cikin gaggawa ba.
Taken wannan shekara shi ne “kwadaitar da jama’a” wajen mayar da hankalinsu kan al’amuran da suka shafi saka mata a harkokin yau da kullum.
Malama Khadija AbdulRa'uf Kuriga, daya daga cikin iyaye matan da ke cikin dimuwar kwashe daliban, ta nuna matukar damuwarta kan rashin sanin halin da sauran daliban ke ciki.
Wani jirgi mai horas da sojojin saman Najeriya ya samu ‘yar karamar matsala a ranar Alhamis, amma matukan jirgin biyu da ke cikin jirgin sun tsira daga hatsarin, in ji rundunar sojin sama.
Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar da takwaransa na Rasha Sergey Lavrov sun tattauna batutuwan da suka shafi moriyar juna da kuma zaman lafiyar yankin a birnin Moscow ranar Laraba.
Rundunar yan-sandan jihar Kaduna ta tabbatar da sace daliban wata makaranta da ke yankin Kurigan a karamar hukumar Chikun, to sai dai ta ce ba ta tantance adadin daliban da aka sace ba yayin da al’ummar garin ke cewa daliban sun kai dari biyu.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan dokar sake fasalin man fetur da iskar gas domin ya sanya Najeriya a matsayin kasar da aka fi son zuba jari a bangaren mai da iskar gas a Afirka.
Majalisar dattawa ta koka kan tabarbarewar harkar tsaro da ya ki ci ya ki cinyewa a Najeriya, ta kuma bayyana cewa, za ta kakkabe rahottani da ta yi tun shekara 2015 domin ta kai wa shugaban kasa saboda a dauki mataki na gaggawa.
Jami’an rundunar shiyyar Maiduguri na Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, ta kama su a ranar Talata, 5 ga wannan watan na Maris.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.