Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya karama zaratan dakarun Rundunar Sojojin Najeriya da wadansu batagari dake kauyen bakin teku suka yiwa kisan gilla da lambar girmamawa na kasa.
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya gana da shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu a fadar aso Villa dake birnin Abuja inda suka tattauna karuwar hare-haren ‘yan bindiga da wasu nau’ukan ta’adanci a jiharsa.
Masana tsaro da sauran jama'a a Najeriya na ci gaba da tsokaci tare da nuna jin dadi, a kan labarin mutuwar kasurgumin ‘dan bindigan nan Dogo Gide da aka tabbatar da mutuwar sa a jihar Sokoto.
Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana amincewar gwamnatinsa na rage wa maniyyatan hajjin bana naira dubu 500 bayan da Hukumar Alhazan Najeriya ta kara naira miliyan 1.9 akan kudin hajjin bana.
Wannan matakin dai na nufin cewa sabon kudin ruwan ya tashi ne daga kaso 22.75 bisa dari da kwamitin MPC ya sanar kusan wata daya da ya gabata da kuma karin shi ne karo na biyu da kwamitin karkashin jagorancin gwamnan Babban Bankin, Olayemi Cardoso ke dauka.
Wata babbar kotu da take Kano a Najeriya ta yankewa ‘dan China Frank Geng-Quangrong da ya kashe Ummulkhulsu Buhari har lahira a shekara 2022 hukuncin kisa ta hanyar rataya
Mawallafin Desert Heral da ke Kaduna, Tukur Mohammed Mamu, ya yi barazanar maka babban lauyan gwamnatin tarayyar Najeriya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), a kotu saboda ayyana shi a jerin masu daukan nauyin ta’addanci a kasar.
Dalibai shida na makarantar Kuriga da aka kubutar daga hannun masu garkuwa da mutane suna jinya a Kaduna, kamar yadda rundunar sojin ta bayyana a jiya.
Babban hafsan tsaron Najeriya Janar Chris Musa ya ce masu ba da bayannan sirri ga sojojin ke kawo cikas ga yaki da kungiyoyin masu garkuwa da mutane da ke ci gaba da sace dalibai da mazauna arewacin kasar.
Gwamnan ya dage kan cewa dalibai 137 da malami daya 'yan-bindigan suka sace kuma gaba daya daliban sun dawao sai dai malaminsu ya rasu a hannun 'yan-bindigan tun a daji.
Kungiyar kare hakkin dan adam ta IHRC-International Human Rights Commission ta shiga jerin masu bukatar majalisa ta sauya matsaya kan dakatar da Sanata Abdul Ningi.
Ofishin mai ba da shawara kan harkokin tsaro (ONSA) ya tabbatar da tserewar manajan yankin Binance na Afirka, Nadeem Anjarwalla daga Najeriya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.