Al’umar garin Kajuru Station sun tabattar wa Muryar Amurka dawowan mutane uku cikin 87 da ‘yan bindiga suka sace a ranar Lahadin da ta gabata.
Fiye da shaguna 180 ne suka kone sakamakon gobarar data tashi a babbar kasuwar Sokoto da sanyin safiyar yau Litinin.
Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya musanta zargin da ake yi wa rundunar sojojin kasar na hannu a kone-konen gidaje a wani kauyen jihar Delta inda wasu matasa suka kashe dakarunta da aka aika aikin wanzar da zaman lafiya.
Kungiyar Manyan Ma'aikatan Jami'o'in Najeriya (SSANU) da takwararta ta Ma'aikatan Da Ba Malamai ba (NASU) sun fara wani yajin aikin gamagari akan abinda suka bayyana da rashin adalci da nuna bambanci wajen biyan bashin albashi daga bangaren gwamnatin tarayya.
Akalla mutane 87 ne ‘yan bindiga suka sake sacewa daga muhallansu bayan wata hari da 'yan bindigan suka kai kauyen Kajuru da ke karamar hukumar Kajuru a jihar Kaduna.
Majalisar Dattawan Najeriya tayi alawadai da mummunan kisan gillar da aka yiwa dakarun aikin wanzar da zaman lafiya na "Operation Delta Safe" su 16 a kauyen Okuama dake karamar hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta.
A ranar Alhamis ne wasu bata-gari suka yi wa wasu dakarun soji kisan gilla lokacin da suke kokarin sulhunta rikici tsakanin kabilar Okuama da Okoloba a Jihar Delta.
Wata babbar kotun tarayya a Najeriya ta yi watsi da daukaka karar bukatar sako bayanan kadarorin tsofaffin shugabannin Najeriya, da suka hada da Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari da mataimakansu Namadi Sambo da Yemi Osinbajo.
Hukumar Kwastan reshen tashan jiragen ruwa ta Tin Can ta kama wasu tarin makamai da kayan soji da alburusai da kuma muggan kwayoyi da aka yi yunkurin shigowa dasu Najeriya ta hanyan sumogal.
Sakamakon yawaitar matsalar satar mutane a Najeriya, gwamnonin arewacin kasar sun amince da yin hadin gwiwa da gwamnatin tarayya da kuma duba yiyuwar yin amfani da wasu hanyoyin na daban wajen shawo kan karuwar matsalar tabarbarewar tsaro da take addabar yankin arewa.
Shugaban kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya bayyana cewar matatar mai ta Fatakwal zata koma bakin aiki a watan Afrilu mai zuwa.
Hukumar NCC mai kula da harkokin sadarwa a Najeriya tace kamfanonin sadarwa na kokarin dawo da sadarwar intanet bayan data katse a jiya Alhamis.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.