Kungiyar Manyan Ma'aikatan Jami'o'in Najeriya (SSANU) da takwararta ta Ma'aikatan Jami'ar da ba Malamai Ba (NASU) sun ayyana shiga yajin aikin gargadi na kwanaki 7 tun daga ranar 18 ga watan Maris din da muke ciki.
A daidai lokacin da aka fara azumin watan Ramadan, Babban Sufeton 'Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya jaddada aniyar rundunar na samar da ingantaccen tsaro ga kowa a fadin Najeriya.
Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa'ad Abubakar III ya sanar da ganin watan azumin Ramadan a Najeriya.
Yayin da al'ummar Musulmi a fadin duniya ke harmar fara azumtar wata mai tsarki na Ramadan, a Najeriya, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, ya ce a fara duban wata daga yau.
Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sace wasu daliban makarantar allo ta almajirao a wani kauye da ake kira Gidan Bakuso a jihar Sokoto da ke Najeriya.
Asusun Tallafawa Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) yayi Allawadai da harin baya-bayan nan da aka kai kan wata makaranta a jihar kaduna.
Shugaban Kasar Najeriya, Bola Tinubu, ya sha alwashin cewar gwamnatinsa zata bada fifiko kan walwalar mata da kiyaye hakkokinsu tare da bunkasa rayuwarsu.
A yayın da ake bukin Ranar Mata ta Duniya a yau Juma’a 8 ga watan Maris na shekarar 2024, wanda aka yiwa taken Zuba jari ga mata: Habaka ci gaba, dubban mata na jan hankali a kan yiyuwar jefa Mata miliyan 340 a duniya cikin tsananin talauci idan ba’a dauki matakan da suka dace cikin gaggawa ba.
Taken wannan shekara shi ne “kwadaitar da jama’a” wajen mayar da hankalinsu kan al’amuran da suka shafi saka mata a harkokin yau da kullum.
Malama Khadija AbdulRa'uf Kuriga, daya daga cikin iyaye matan da ke cikin dimuwar kwashe daliban, ta nuna matukar damuwarta kan rashin sanin halin da sauran daliban ke ciki.
Wani jirgi mai horas da sojojin saman Najeriya ya samu ‘yar karamar matsala a ranar Alhamis, amma matukan jirgin biyu da ke cikin jirgin sun tsira daga hatsarin, in ji rundunar sojin sama.
Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar da takwaransa na Rasha Sergey Lavrov sun tattauna batutuwan da suka shafi moriyar juna da kuma zaman lafiyar yankin a birnin Moscow ranar Laraba.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.