Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wannan Wata Za A Fara Tonon Albarkatun Man Fetur A Kolmani – Mele Kyari


Malam Mele Kyari Shugaban kamfanin NNPCL
Malam Mele Kyari Shugaban kamfanin NNPCL

A watan Fabrairun da mu ke ciki ne ake sa ran za a fara tonon albarkatun man fetur da iskar gas da aka samu a Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe.

Dan Majalisar Dattawa mai wakiltar shiyyar Bauchi ta kudu, Sanata Shehu Buba ne ya bayana hakan yayin da yake tattaunawa da gidan rediyon sashen Hausa na Muryar Amurka a Bauchi.

Yace Manajan Darektan kamfanin NNPCL, Mele Kyari, ne ya shaidawa masa da Mai Bada Shawara Kan Sha’anin Tsaro na Kasa, Malam Nuhu Ribadu yayin da suka ziyarci ofishin kamfanin a Abuja.

A cewarsa, Manajan Daraktan ya ba da tabbacin cewa kamfanin da aka baiwa aikin hakar albarkatun man fetur din daga kasar Indiya ya iso Najeriya don fara
aiki gadan gadan a cikin wannan watan Fabrairu.

Ga cikakken rahoton Muhammad Abdulwahab:

Wannan Wata Za A Fara Tonon Albarkatun Man Fetur A Kolmani - Mele Kyari
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:06 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG