A cewar Onanuga, ziyarar shugaban zuwa kasar da ke nahiyar Turai ta kashin kai ce, inda ya kara da cewa Tinubu zai yi ziyarar ne a kan hanyarsa ta zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha
Karin kasafin kudin ya samo asali ne sakamakon samun karin kudin shiga na Naira tiriliyan 1. 4 daga hukumar tara kudaden shiga ta Najeriya (FIRS), da Naira tiriliyan 1.2 daga hukumar yaki da fasakwabrin kasar (NCS) da kuma Naira tiriliyan 1.8 da sauran hukumomin gwamnati suka tara.
Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara wadda ta tabbatar da faruwar Lamarin ta bakin jami’in hulda da jama’a na Rundunar DSP Yazid Abubakar yace mutane 17 ne suka mutu yayin da wasu 17 suke kwance a asibiti suna samun kulawar likitoci.
Duk da jinkirta matakin a wasu fannoni, har yanzu akwai fargaba akan abin da zai kasance nan gaba a bangaren tallafin da Amurka ke bayarwa a fannin lafiya a fadin duniya.
Baya ga mutuwar mutane, hatsarin ya kuma sabbaba mutuwar kimanin shanu 15 da awaki fiye da 20.
Satar danyen man da ake yi tsawon shekaru ta janyowa kasar asarar da aka kiyasta cewar ta kai ganga miliyan 701.48 tun a shekarar 2009, lokacin da NEITI ta fara bin diddigin asarar da aka yi.
Bayan tattaunawa mai tsawo, bangarorin 2 sun amince da kafa wani kwamiti mai wakilai 10 da zai kunshi mutum 5 daga bangaren gwamnatin Najeriya sai mutum 5 daga bangaren NLC su sake nazarin binciken tare da mika rahoto cikin makonni 2.
A makon daya gabata, ma’aikatar lafiya ta Uganda ta tabbatar da barkewar annobar da ta yi sanadiyar mutuwar mutum guda yanzu kuma take bin sawun mutane 44 da ya yi mu’amala da su.
Al’amarin wanda ya faru a Lahadin da ta gabata ya biyo bayan samun bayanan sirrin da rundunar sojin Najeriya ta yi.
Tems wacce ainihin sunanta shine Temilade Openiyi ta lashe kyautar fitacciyar waka daga nahiyar Afrika mai taken “love me jeje,” inda tayi takara da mawakan Najeriya irinsu Davido da Yemi Alade da Asake da Wizkid da Lojay da kuma Burna Boy.
Ana zargin tsohon shugaban hukumar NHIS ne da yin amfani da mukami wajen baiwa kansa damar da ba ta dace ba tsakanin shekarar 2016 zuwa 2017.
Saukin farashin da aka samu, ya dace da faduwar farashin man fetur a kasuwar duniya, sannan, kamfanin na Dangote, yana so talakwan Najeriya suma su ci moriyar saukin farashin da aka samu, domin su samu saukin tsadar rayuwar da ake fama da ita.
Domin Kari
No media source currently available