Yayin bikin mika ginin da zai zamo shelkwatar aikin wanzar da zaman lafiyar a hukumance, Gwamna Lawal Dauda ya jaddada aniyar gwamnatinsa ta tallafawa hukumomin tsaro wajen yaki da laifuffuka.
Masu zanga-zangar na dauke da kwalaye da suka rubuta korafe-korafensu.
Duk da komawa yanar gizo da wasu kafafen ke yi hakan bai rage martabar akwatin rediyo ba da ya zama tamkar al'ada a tsakanin al'umma musamman na arewacin Najeriya.
Karin hasken na zuwa ne kwanaki bayan da kwamitin Majalisar Dattawa akan asusun ajiyar gwamnati ya bayyana tsananin damuwa game da al’amura da dama dake da nasaba da rundunar ‘yan sandan Najeriya, ciki har da almundahanar kudade da batan makamai.
Shugaban bankin raya kasashen Afirka (AFDB), Akinwunmi Adesina, ya musanta rahotannin da ke danganta shi da takarar shugabancin Najeriya a shekarar 2027.
Yayin da Turai ke fadi tashin neman iskar gas da za ta maye gurbin ta Rasha, an sake farfado da shirin tura iskar gas din daga Najeriya zuwa Turai.
Gwamnatin jihar Borno ce ta dauki nauyin aikin dawo da mutanen gida da hadin gwiwar kasar Chadi da hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNHCR), biyo bayan rattaba hannu a kan yarjejeniyar dawo dasu gida a makon daya gabata a lardin Lac na kasar Chadin.
Duk da yarjejeniyar, kamfanonin sadarwar sun ci gaba da aiwatar da karin, abinda ya sabbaba NLC ba da wa’adin 1 ga watan Maris domin tsayar da ayyukanta matukar ba’a janye karin ba.
A baya-bayan nan, matatar mai zaman kanta ta zaftare tsohon farashin daukar fetur na Naira 950 zuwa 890 “duba da halin da kasuwa ke ciki”.
Kudurorin sun hada dana dokar harajin Najeriya ta 2024 da kudirin gudanar da haraji dana kafa hukumar tattara harajin Najeriya da kuma na kafa hukumomin tattara haraji na hadin gwiwa.
Majalisar ta kuma koka da rashin ingancin ayyukan kamfanonin sadarwa inda ta jaddada cewar bai kamata su yi karin kudin kiran waya da sayen data ba har sai sun inganta ayyukansu.
Domin Kari
No media source currently available