Gwamnatin jihar Borno ce ta dauki nauyin aikin dawo da mutanen gida da hadin gwiwar kasar Chadi da hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNHCR), biyo bayan rattaba hannu a kan yarjejeniyar dawo dasu gida a makon daya gabata a lardin Lac na kasar Chadin.
Duk da yarjejeniyar, kamfanonin sadarwar sun ci gaba da aiwatar da karin, abinda ya sabbaba NLC ba da wa’adin 1 ga watan Maris domin tsayar da ayyukanta matukar ba’a janye karin ba.
A baya-bayan nan, matatar mai zaman kanta ta zaftare tsohon farashin daukar fetur na Naira 950 zuwa 890 “duba da halin da kasuwa ke ciki”.
Kudurorin sun hada dana dokar harajin Najeriya ta 2024 da kudirin gudanar da haraji dana kafa hukumar tattara harajin Najeriya da kuma na kafa hukumomin tattara haraji na hadin gwiwa.
Majalisar ta kuma koka da rashin ingancin ayyukan kamfanonin sadarwa inda ta jaddada cewar bai kamata su yi karin kudin kiran waya da sayen data ba har sai sun inganta ayyukansu.
A jiya Talata ne Ganduje yayi wannan furuci a sakatriyar jam’iyyar APC ta kasa a Abuja, a sa’adda ya karbi bakoncin mambobin kungiyar matasan Arewa masu goyon bayan Tinubu
Najeriya ta haura matsayi biyar a cikin shekarar bara ta 2024, inda ta tashi daga matsayi na 145 zuwa 140 a cikin kasashe 180 na duniya bayan da ta samu maki daya a cikin sabuwar kididdigar.
Karin wani bangare na karin kaso 50 cikin 100 na harajin kiran waya da sayen data, da hukumar kula da harkokin sadarwa ta Najeriya (NCC) ta amince da shi saboda halin da kasuwa ke ciki a halin yanzu.
Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Muhammad Idris, ne ya sanar da umarnin yayin ganawa da manema labarai a Abuja a yau Talata.
Babban daraktan hukumar samar da lantarki a karkara (REA), Abba Aliyu, yace da zarar Shugaba Bola Tinubu ya zartar da kasafin kudin zuwa doka, hukumarsa za ta fara aikin samar da lantarki a makarantun gwamnatin.
Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta bayyana cewar ta samu nasarori a yakin da take yi shan miyagun kwayoyi, musamman da hadin gwiwar jihohi da kananan hukumomi.
A watan Yunin 2021 aka dawo da Kanu zuwa Najeriya kuma tun lokacin yake tsare tare da fuskantar shari'a a kan zargin ta'addanci.
Domin Kari
No media source currently available