Yayin da Shugaba Trump ke ta lafta haraji kan kayakin kasashen waje, a gefe guda kuma ya bukaci a rage kudin ruwa a cikin gida don saukaka hada hada.
Trump ya nanata ikirarin da yayi a lokacin yakin neman zabensa na 2024 cewar FEMA ta kashe miliyoyin daloli cikin rashin adalci a martaninta ga mummunar guguwar da ta afkawa jihar North Carolina a watan Satumban da ya gabata, inda ta hallaka fiye da mutane 100.
Sallamar Paul Martin na zuwa ne kwana guda bayan da ofishinsa ya fitar da wani rahoto da ya caccaki yadda gwamnatin Trump ke kokarin wargaza hukumar.
Dusar kankarar mafi yawa da ake hasashe ta sauka zata kai centimita 25, wanda ake hasashen zai kasance a wani yankin arewaci da tsakiyar jihar Virginia da gabashin yammacin Virginia
Yana zargin cewa tsauraran matakan kauce ma bayar da cin hanci da rashawa ga jami'an kasashen waje da aka gindaya ma Amurkawa, na hana kasuwancin Amurka gogayya a kasuwannin duniya.
Shugaban na Amurka ya nuna alamar cewa ba zai sauya matsaya ba game da shirin Amurka na karbe iko da Gaza tare da debe firgitattun mazauna cikinta da kuma sauya yankin da yaki ya daidaita.
An gano wasu yara da shekarun su basu wuce na yara yan makaranta ba, a wani karamin gari a Arewacin Texas ta Amurka su 15 dauke da cutar kyanda, da ya kasance koma baya wajen samun rigakafi a jihar.
A ranar Litinin ma'aikatar shari’a ta umurci masu gabatar da kara na tarayya a New York da su yi watsi da tuhume tuhumen da akewa magajin garin New York Eric Adams, cewar wata takarda da ta fito daga mukaddashin babban mai shari’a Emil Bove.
Trump ya maida batun zaftare kasafin kudin gwamnatin tarayyar Amurka wani babban jigo na gwamnatinsa, inda aka dorawa tawagar DOGE karkashin jagorancin attajiri Elonk Musk alhakin bankado yadda ake kashe kudaden gwamnati.
An yi bukin bude taron da ya tuna da mutanen da suka mutu da wadanda suka ji rauni a mumunnan harin da aka kai wa mutane da motar akori kura a ranar sabuwar shekara a shahararren titin Bourbon a birnin New Orleans.
Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz, ya ce idan Amurka ta kuskura ta kakaba wa tarayyar Turai haraji, a shirye Turai take ita ma ta mai da martani “cikin sa’a daya,”
Domin Kari
No media source currently available