Shugaban na Amurka ya nuna alamar cewa ba zai sauya matsaya ba game da shirin Amurka na karbe iko da Gaza tare da debe firgitattun mazauna cikinta da kuma sauya yankin da yaki ya daidaita.
An gano wasu yara da shekarun su basu wuce na yara yan makaranta ba, a wani karamin gari a Arewacin Texas ta Amurka su 15 dauke da cutar kyanda, da ya kasance koma baya wajen samun rigakafi a jihar.
A ranar Litinin ma'aikatar shari’a ta umurci masu gabatar da kara na tarayya a New York da su yi watsi da tuhume tuhumen da akewa magajin garin New York Eric Adams, cewar wata takarda da ta fito daga mukaddashin babban mai shari’a Emil Bove.
Trump ya maida batun zaftare kasafin kudin gwamnatin tarayyar Amurka wani babban jigo na gwamnatinsa, inda aka dorawa tawagar DOGE karkashin jagorancin attajiri Elonk Musk alhakin bankado yadda ake kashe kudaden gwamnati.
An yi bukin bude taron da ya tuna da mutanen da suka mutu da wadanda suka ji rauni a mumunnan harin da aka kai wa mutane da motar akori kura a ranar sabuwar shekara a shahararren titin Bourbon a birnin New Orleans.
Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz, ya ce idan Amurka ta kuskura ta kakaba wa tarayyar Turai haraji, a shirye Turai take ita ma ta mai da martani “cikin sa’a daya,”
Shugabannin Republican da na Democrat a kwamitocin kasafin kudi guda biyu a Majalisa sun gudanar da tattaunawa kan kudirin kashe kudin gwamnati a karshen watan Janairu, hadimai sun ce bangarorin biyu sun kuduri aniyar cimma matsaya. Sai dai fatan alheri yana dushewa a 'yan kwanakin nan.
Kasuwannin hannayen jari a Amurka sun yi kasa a ranar Juma'a yayin da ake nuna damuwa game da hauhawar farashin kayayyaki da haraji, yayin da wani rahoto da aka sa ido sosai akai ya ba da mabanbancin ma’ana game da kasuwar aikin yi a Amurka.
Masu aikin ceto a jihar Alaska sun ci gaba da bincike ya zuwa ranar Juma’a na wani jirgin sama da ya bace a ranar Alhamis da mutane 10 a ciki, da suka hada da fasinjoji 9 da matuki guda.
Shugaban Amurka Donald Trump ya fada a jiya Jranar cewa ya kamata a kalli shirinsa na neman mallakar Zirin Gaza, a matsayin mai hada hadar gine-ginen gidaje, inda kasar zata zuba jari a wani bangare na duniya amma bata bada lokacin gudanar da aikin ba, yana mai cewa bama gaggawa a kai.
Hukumar kashe gobarar Nome tace “matukin jirgin ya shaidawa hasumiyar kula da zirga-zirgar jiragen sama cewar yana niyar sanya jirgin a tsarin jira yayin da yake jiran titin saukar jiragen ya zama babu komai akai” gabanin bacewarsa.
A yau Alhamis Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewar Isra’ila zata mikawa kasarsa iko da Gaza bayan lafawar rikici tare da tsugunar da al’ummar zirin a wani wuri na daban, abinda yace ba zai bukaci tura dakarun sojin Amurka zuwa yankin ba.
Domin Kari
No media source currently available