Shugaba Donald Trump ya ba da umarnin dakatarwa da kuma yin nazari a kan wata doka, wace ta gindaya sharadin harkar kasuwancin Amurka a kasashen waje a tsawon shekaru hamsin, yana zargin cewa tsauraran matakan kauce ma bayar da cin hanci da rashawa ga jami'an kasashen waje da aka gindaya ma Amurkawa, na hana kasuwancin Amurka gogayya a kasuwannin duniya.
“(Jinkirta dokar) zai haifar da karin harkokin kasuwanci ga Amurka," a cewar Trump, yayin da ya sanya hannu a ranar Litini, kan umurnin sanya Ma’aikatar Shari’a ta dakatar da jerin binciken da ta keyi, sannan kuma ta yi nazarin Dokar Hana Aikata Rashin Gaskiya a Kasuwanci a Kasashen Waje, ta 1977 na tsawon watanni shida masu zuwa.
Umarnin na cewa "rashin daidaito da kuma saurin aiwatar da Dokar, wace ake kira FCPA a takaice, da ya shafi 'yan kasar Amurka da kamfanonin su– ta wajen Gwamnatin mu – kan al'adun kasuwanci na yau da kullum a wasu ƙasashe, ba kawai yana janyo barnata dan kayan aikin da ake da shi ba ne, wanda za a iya amfani da shi wajen mayar da hankali kan kiyaye 'yancin Amurka ba, har ma yana gurgunta Amurka wajen gogayyar tattalin arziki, wato kenan, har da tsaron kasa."
Dandalin Mu Tattauna