Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Trump Yayi Umarnin Dakatar Da Wata Dokar Kasuwanci Da Kasashen Waje


US President Donald Trump speaks to the press after signing an executive order, alongside US Secretary of Commerce nominee Howard Lutnick (R), in the Oval Office of the White House in Washington, DC, on February 10, 2025. (Photo by ANDREW CABALLERO-REYN
US President Donald Trump speaks to the press after signing an executive order, alongside US Secretary of Commerce nominee Howard Lutnick (R), in the Oval Office of the White House in Washington, DC, on February 10, 2025. (Photo by ANDREW CABALLERO-REYN

Yana zargin cewa tsauraran matakan kauce ma bayar da cin hanci da rashawa ga jami'an kasashen waje da aka gindaya ma Amurkawa, na hana kasuwancin Amurka gogayya a kasuwannin duniya.  

Shugaba Donald Trump ya ba da umarnin dakatarwa da kuma yin nazari a kan wata doka, wace ta gindaya sharadin harkar kasuwancin Amurka a kasashen waje a tsawon shekaru hamsin, yana zargin cewa tsauraran matakan kauce ma bayar da cin hanci da rashawa ga jami'an kasashen waje da aka gindaya ma Amurkawa, na hana kasuwancin Amurka gogayya a kasuwannin duniya.

“(Jinkirta dokar) zai haifar da karin harkokin kasuwanci ga Amurka," a cewar Trump, yayin da ya sanya hannu a ranar Litini, kan umurnin sanya Ma’aikatar Shari’a ta dakatar da jerin binciken da ta keyi, sannan kuma ta yi nazarin Dokar Hana Aikata Rashin Gaskiya a Kasuwanci a Kasashen Waje, ta 1977 na tsawon watanni shida masu zuwa.

Umarnin na cewa "rashin daidaito da kuma saurin aiwatar da Dokar, wace ake kira FCPA a takaice, da ya shafi 'yan kasar Amurka da kamfanonin su– ta wajen Gwamnatin mu – kan al'adun kasuwanci na yau da kullum a wasu ƙasashe, ba kawai yana janyo barnata dan kayan aikin da ake da shi ba ne, wanda za a iya amfani da shi wajen mayar da hankali kan kiyaye 'yancin Amurka ba, har ma yana gurgunta Amurka wajen gogayyar tattalin arziki, wato kenan, har da tsaron kasa."

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG