Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Al’ummar Rivers Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Malalar Mai


Masu zanga-zanga a jihar Ribas
Masu zanga-zanga a jihar Ribas

Masu zanga-zangar na dauke da kwalaye da suka rubuta korafe-korafensu.

Al’ummar garin Ogale dake karamar hukumar Eleme ta jihar Rivers sun gudanar da zanga-zanga a kan matsalar malalar mai da suke zargin reshen kamfanin mai na Shell da haddasawa.

Masu zanga-zangar na dauke da kwalaye da suka rubuta korafe-korafensu.

Masu zanga-zanga a jihar Ribas
Masu zanga-zanga a jihar Ribas

A ranar 5 ga watan Fabrairun da muke ciki reshen kamfanin Shell na Najeriya ya ba da rahoton samun malalar mai a Ogale, kusa da birnin Fatakwal, lokacin da wani ramin tattara dagwalo ya yi ambaliya yayin aikin wanke bututu.

Masu zanga-zanga a jihar Ribas
Masu zanga-zanga a jihar Ribas

Kamfanin ya kara da cewa tawagar karta kwana a kan malalar ta yi martani tare da tsayar da ambaliyar da kuma sanar da hukumomi, inda ya kara da cewa ana tsare-tsare a kan yadda wata tawaga karkashin jagorancin masu sanya idanu za ta nazarci musabbabi da kuma tasirin malalar man.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG