Wani jirgin mai lamba N580KR , dauke ne da wasu muhimman mutane da kawo yanzu ba a bayyana sunayesu ba, ya yi hadari a Ibadan, babban birnin jihar Oyo a kudu maso yammacin Najeriya.
A wani mataki da kotun kolin Najeriya ta yanke, ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar da aka yankewa tsohon dan majalisar wakilai Farouk Lawan, bisa samunsa da laifin cin hanci da rashawa.
Bayanai sun nuna cewa bayan wadanda 'yan bindigar suka kashe hakama sun yi garkuwa da wasu da ba a san adadin su ba.
Kamfanin makamashi na “Mainstream” a Najeriya, wanda tuni yake gudanar da manyan tashoshin samar da wutar lantarki guda biyu a kasar, ya fara gudanar da wani sabon ginin da kasar China ta samar, kusan shekara guda bayan samun wannan damar in ji kamfanin a jiya.
Gwamnatin Bayelsa ta ce za ta ba da fifiko kan koyo da koyar da harsunan Ijaw, da Faransanci, da kuma Sinanci a makarantun gwamnati a jihar.
Kotun kolin Najeriya ta yi watsi da karar da dan takarar jam’iyyar APC, Tonye Cole ya daukaka inda ya kalubalanci nasarar Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP a matsayin zababben gwamnan jihar Ribas a bisa rashin cancanta.
Sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya hallarci wani taro da bankin raya Afurka ya shirya a birni Legas na samar da abinci da kuma tallafa wa manoman nahiyar.
Mai martaba Sarkin Keffi, Alhaji Shehu Yamusa III, ya ce mayarwa sarakunan gargajiya wadansu ikon su na da daya daga inda za’a sami nasara a yaki da matsalolin tsaro.
Ziyarar na da nufin karfafa alakar da ke tsakanin Amurka da Najeriya da kuma lalubo damar yin hadin gwiwa a bangarori daban-daban.
Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ta Najeriya ICPC, Dr. Musa Adamu Aliyu, SAN, ya bukaci daliban kasar da su tashi tsaye domin daukar nauyinsu a matsayin masu kawo sauyi da Najeriya ke matukar bukata wajen dakatar da cin hanci da rashawa musamman a makarantu.
Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken, ya gana da shugaban Najeriya Bola Tinubu a yau Talata a fadar gwamnati dake Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.