Kungiyoyin dai sun yi kira da a hukunta duk wanda aka samu da hannu cikin lamarin domin ya zama izina ga wasu.
Kungiyar tuntuba ta dattawan Arewa ACF, ta koka kan yadda ba’a zartar da hukuncin da ya kamata kan mutanen da ke da hannu akan matsalolin satar yara da akan yi safarar su daga yankin arewacin Najeriya zuwa kudanci domin sayar da su.
Kamfanin na Dangote ya kara da cewa har ya turawa EFCC wasu bayanai a mataki na farko, amma jami’an hukumar suka ki karbar bayanan suka kuma matsa cewa sai sun kai ziyara hedkwatar kamfanin.
Shugaba Tinubu ya ce zasu yi iya kokarinsu domin ganin an hanzarta inganta wutar lantarkin da duk dan kasa zai mora.
Akeredolu ya yi fama da cutar daji tsawon watanni wanda hakan ya sanya shi kwantawa a asibitin Jamus inda rai ya yi halinsa a ranar 27 ga watan Disambar 2023.
Rahotanni sun nuna cewa, kona gidan basaraken ya biyo bayan kisan gillar da aka yi a jajibirin Kirsimeti da ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 160.
Masana tattalin arziki sun ce samame da jami'an hukumar EFCC su ka kai shalkwatar rukunin kamfanonin Dangote a Legas, a ranar Alhamis, ka iya shafar farashin hannayen jari na kamfanonin, amma ba zai shafi hada hadar sarrafawa da kuma farashin kayayyakin na Dangote ba a kasuwannin duniya.
Wannan harin dai ya yi matukar tada hankalin mazauna wannan yakin da ke da yawan jama’a da zirga-zirgar ababen hawa.
Gwamnan jihar Filato, Caleb Manasseh Mutfwang, ya shaidawa kotun koli jiya cewa, kotun daukaka kara ba ta yi masa adalci ba wajen soke zabensa.
Hamshakin dan kasuwa, dan asalin kasar Afrika ta Kudu, Johann Rupert ya sha gaban attajirin dan kasuwa Aliko Dangote inda ya zama wanda ya fi kowa arziki a nahiyar Afirka, kamar yadda mujallar Forbes ta fitar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.