A wani kakkausan martani da ta mayarwa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu game da jawabin sa na sabuwar shekara, jam’iyyar PDP ta bayyana shi a matsayin yaudara, da’awar karya, da alkawuran da baza’a iya cika su ba, inda ta bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta kasa magance matsalolin da ke addabar al’umma.
Dan takaran Shugaban Kasa a karkashin tutar babbar jam’iyar adawa ta NDC a zaben 2024, kuma tsohon Shugaban Kasa, John Dramani Mahama, ya ba da tabbacin cewa, a shirye yake ya ba Musulman kasar karin hutun bukukuwan Idi, idan jam’iyarsa ta samu nasara a zabe mai zuwa.
Matasan yankin Sahel sun gudanar da taro da nufin tattauna a kan manyan kalubalen da suke cin karo dasu a wannan yanayi da kasashen uku dake yankin Sahel ke fama da matsalolin da suka dabaibaye su.
A wani martani mai ratsa zuciya da ya yi dangane da mummunar asarar rayuka da aka yi a jajibirin Kirsimeti a Najeriya, Fafaroma Francis ya mika addu’o’i da ta’aziyya ga iyalan da wani mummunan hari da aka kai jihar Filato ya rutsa da su.
Fasinjoji 163, 878 ne suka ci gajiyar wannan tallafin sufurin na lokacin bukuwan Kirsimeti da hutun karshen shekara na shugaban kasa a cikin kwanaki 10 na farkon shirin.
Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya ce kashe-kashen dake aukuwa a jihar ta'addanci ne tsantsa da wasu ke aikatawa akan jama'ar jihar, kuma dole a tinkare shi akan ayyukan ta'addanci, idan har ana so a yi nasarar dakatar da kisan mutane da barnata dukiyoyi.
A wannnan Shekarar da aka yi bankwana da ita ta ne wata matar aure, Hafsa Surajo, da a ke zargi da kashe abokin sana’arta ta hanyar caccaka masa wuka, alammarin da ya ja hankalin jama’a.
A jawabinsa na sabuwar shekara na farko tun bayan hawansa mulki a watan Mayun 2023, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi jawabi ga al’ummar kasar, inda ya sanar da fara aiwatar da sabon albashin ma’aikata na kasa a cikin sabuwar shekara.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kaddamar da wata runduna ta musamman da za ta yi yaki da batagari da ke kashe-kashen rayuka da barnata dukiyoyin jama’a a jihar Filato.
Mataimakin shugaban Kwamitin Kasafi na Majalisar Dattawa, Sanata Mohammed Ali Ndume, ya ce sun yi aiki tukuru, ba dare ba rana domin sun gano wurin da aka yi ta jita-jita cewa, an fifita yankin kudu kan yankin arewa a kasafin kudin 2024.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.