Rundunar ‘Yan Sandan jihar Neja ta tabbatar da ceto hudu daga cikin mutane 17 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su daga dajin Kpakuru da ke garin Kagarko a jihar Kaduna da kuma kauyen Chachi na karamar hukumar Tafa.
Gamayyar Kungiyoyin Arewa Ta Kira Taron Gaggawa a Abuja game da matsalar tsaro.
Mai shari’a James Omotosho na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya soke kasafin Naira biliyan 800 da kungiyar ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas karkashin jagorancin Edison Ehie ta amince da shi da kuma sanya hannun gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara.
Shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayar da takardar shedar karramawa ga tsohuwar jami’ar sojin saman Amurka, Sarauniya Irene Olasumbo Cole, ‘yar asalin Najeriya, domin sadaukar da kai da ta yi wajen yi wa kasa hidima a rundunar sojin kasar Amurka.
Hajiya Inna Galadima ta jam'iyyar APC, ta zama zababbiyar shugabar karamar hukumar Jere ta jihar Borno, ta kasance Shugabar Karamar Hukuma mace ta farko a jihar.
Gwamnatin jihar Legas a Najeriya ta rufe kasuwar Oke-Afa, Isolo, da Katangua, Abule Egba, bisa karya ka’idojin zubar da shara, da suka hada da rashin tsaftar muhalli a kasuwannin, wadanda ke haifar da munanan laifuka na muhalli.
“Muna muku godiya saboda labaru masu inganci da kuke ba mu, wannan gidan rediyo naku yana da babban aminci. Gidan rediyo ne da kasashenmu na Afirka suke amfani da shi.” Shugaban kungiyar kare hakkin dan adam ta CODDAE a Nijar, Alhaji Moustapha Kadi.
Bayanai na nuni da cewa hakan na faruwa ne yayin da matsalar ta rashin tsaro ke raguwa a arewa maso yammcin kasar, kamar a yankunan jihar Sokoto.
Za ta kafa tarihi a watan Mayu, bayan da abokan aikinta baki danayansu suka zabe ta a matsayin Magajiyar garin Leeds a Burtaniya.
Kotun koli ta yi watsi da karar da dan takarar gwamna karkashin inuwar jam’iyyar PDP, David Umbugadu ya shigar kan nasarar gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa a yau Juma’ah.
Kotun koli ta yi watsi da karar da dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Isah Ashiru ya shigar na kalubalantar nasarar gwamna Uba Sani na jihar Kaduna a zaben shekarar 2023.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.