Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wadanda Suka Yi Garkuwa Da Shugaban PDP Na Jihar Legas Sun Nemi A Biya Su Miliyan 200


Tutar Jam'iyyar PDP
Tutar Jam'iyyar PDP

Masu garkuwa da mutane sun bukaci a biya Naira miliyan 200 kudin fansa domin sako shugaban PDP na Legas da suka sace.

A daren ranar Alhamis ne wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shugaban jam’iyyar PDP na jihar Legas, Philip Aivoji, a hanyar Legas zuwa Ibadan, a lokacin da yake dawowa daga taron jam’iyyar na shiyyar Kudu-maso-Yamma a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Dan takarar gwamnan jihar Legas a karkashin jam’iyyar PDP a zaben 2023, Dr. Abdul-Azeez Adediran, ya bayyana kaduwarsa da labarin sace shugaban jam'iyyar a kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.

Adediran ya bayyana lamarin a matsayin wani abu mai daure kai ga karuwar rashin tsaro a Najeriya musamman a yankin Kudu maso Yamma.

Ya dora alhakin hakan kan gazawar gwamnati a fannin tsaro, duk da cewa hakan ya jefa rayuwar ‘yan kasa cikin hadari, don haka ya bukaci daukar matakin gaggawa daga jami’an tsaro domin a gaggauta sakin shugaban jam’iyyar da aka sace.

Ya kuma shawarci jami’an tsaro na yankin, Amotekun su hada kai da ‘yan sanda a wannan aikin ceto.

A gefe guda kuma rahotanni daga Najeriyar na cewa rundunar jihar Oyo ta ce tan kan bibiyar mutanen da suka yi garkuwa da shugaban jam'iyyar ta PDP a cewar jaridar Daily Trust.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG