Jirgin ya kau wa hanyarsane a lokacin da yake kokarin sauka a Ibadan da ga birnin abuja.
Rahotannin dake fitowa daga kusa da filin jirgin saman na Ibadan sun nuna cewa mutane goma ne suke cikin jirgin kuma babu wanda ya mutu ko yayi rauni.
Tuni dai jamian kashe gobara suka garzaya wajen hadarin don hana tashin wuta da kulawa da fasinjojin.
Kakakin Hukumar Kula da Jiragen Saman Najeriya Carol Adekotujo wadda ya tabbatar da hadarin yace sun tura jamiansu wajen don binciken dalilin hadarin
Ga cikkaken rahoton Hassan Umaru Tambuwal daga Ibadan, Babban birnin jihar Oyo.
Dandalin Mu Tattauna