Yayin da gwamnatin Najeriya ke cewa tana daukar matakai domin bunkasa ayukkan kasuwanci da habaka tattalin arziki, wasu 'yan kasuwa na kokawa akan cewa har yanzu suna fuskantar kalubale da ke yin tarnaki ga kasuwanci da kuma tattalin arzikinsu.
Attajirin dan kasuwa, Aliko Dangote, ya kwato matsayinsa na attajirin da ya fi kowa arziki a nahiyar Afirka, kamar yadda mujallar Forbes ta bayyana.
Kotun kolin Najeriya ta jingine hukunci a karar da gwamnan jihar Filato Caleb Mutfwang ya shigar inda ya bukaci ta tabbatar da zabensa.
Sabbin matakan za su yi tasiri ga tafiye-tafiyen manyan jami’an gwamnati da suka hada da Shugaban Kasa, Mataimakin Shugaban Kasa, da kuma Uwargidan Shugaban Kasa.
Kwana daya bayan da shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Ministar jin ƙai, Betta Edu, ta bayyana a ofishin hukumar EFCC mai yaki da cin hanci da rashawa a Abuja kan zargin ta da bada umurnin tura kudi kimanin naira miliyan 585 zuwa asusun banki na wata mata.
Al’ummar Kiristocin Jihar Filato sun yi tattaki zuwa gidan gwamnatin Jihar da ke birnin Jos domin tunawa da mummunan asarar rayuka da aka yi a cikin 'yan kwanakin nan.
Wadanda aka sallama sun hada da Babatunde Irukera, shugaban hukumar kula sahihancin ayuka da kayayyaki (FCCPC), da Alexander Okoh, shugaban hukumar kula da harkokin gwamnati (BPE).
Gwamnatin Tarayya na dab da fara aiwatar da shirinta na tillastawa hukumomi da ma’aikatun gwamnati ware kaso 5 cikin 100 na guraben aikin yi ga masu bukata ta musamman a fadin Najeriya.
Wasu sarakuna da suka hada da 'yan majalisar Sarkin musulmi na dakon fuskantar hukunci, sakamakon wani kwamiti da gwamnatin Sakkwato ta kafa don gudanar da bincike akan zarginsu da aikata laifuka masu alaka da siyasa.
Sama da kwanaki 100 da sace daliban Jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau na jihar Zamfara, iyayen yaran sun sake kaiwa gwamnati kokensu don ta kara kaimi wajen biyan bukatun da ‘yan ta’addan suka gabatar na musayar mutanensu dake tsare a hannun gwamnati da ‘ya’yansu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.