Gobarar, da ta tashi cikin dare a kasuwar Panteka tsohowa dake cikin garin Kaduna, ta lakume rumfunan masu sayar da katako sama da hamsin kafin zuwan 'yan kwana-kwana wadanda su ka kashe ta.
Mazauna birnin Ibadan, a jihar Oyo da ke kudu maso yammacin Najeriya, mai yawan jama'a sun ji karar fashewar wani abu mai karfi da misalin karfe 7:45 na dare, lamarin da ya haifar da firgici yayin da da dama suka tsere daga gidajensu.
Hukumar NDLEA mai hana sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya, ta bayyana damuwa kan yadda matasa a jihar Kano ke mayar da magungunan wasu cututtuka a matsayin ababen sanya maye.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fada ranar Talata cewa gwamnatinsa za ta fara "gagarumin shirin ilimantarwa" ga matasa a matsayin daya daga cikin hanyoyin magance karuwar satar mutane don neman kudin fansa da ke barazana ga babban birnin kasar tare da yankunan Arewacin kasar da ke fama da rikici.
Ministan babban birnin Tarayyar Najeriya, Barrister Nyesome Wike ya jagoranci wani taron tsaro na gaggawa da ya kunshi baki dayan manyan kusoshin tsaron birnin.
Hukumar ba da agajin gaggawa ta Najeriya ta sanar a jiya Talata cewa fasinjoji takwas ne aka tabbatar sun mutu, sannan kimanin wasu 100 kuma sun bace, bayan kifewar kwale-kwalen da suke ciki a arewa maso tsakiyar kasar.
Kamfanin Shell ya fada a ranar Talata cewa ya cimma matsayar sayar da kasuwancinsa na teku a yankin Niger Delta na Najeriya ga wata hadakar kamfanoni, a wata yarjejeniya da ta kai dala biliyan 2.4.
Hakan na kunshe ne a cikin rahoton hukumar kididdigar na watan disambar shekarar 2023 dake bin diddigin hauhawar farashin kayayyakin masarufi da aka fitar a jiya litinin.
A wani rahoton da Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta jihar Neja ta fitar a karshen shekara ta 2023 ya nuna cewa da ga shekarar 2017 zuwa wannan lokaci sama da garuruwa 335 ne Mutanensu suka tarwatse a cikin kananan Hukumomi 14 na jihar Nejan saboda Matsalar Hare Haren yanfashin Dajin
Kotun kolin Najeriya ta jingine yanke hukuncin kan karar kujerar gwamnan jihar Nasarawa, zuwa wata rana da zata sanar nan gaba.
Uwargidan shugaban kasar Najeriya Remi Tinubu, ta bi sahun jama'ar da suka yi tir da Allah wadai da kisan wata daliba da aka sace tare da wasu 'yan uwanta mata guda biyar, inda ta bayyana hakan a matsayin "mummunan rashi".
Matatar man fetur mafi girma a nahiyar Afirka ta fara aiki a Najeriya, kamar yadda kamfanin ya bayyana, wanda ya kawo karshen tsawon shekaru da aka kwashe ana jiran soma aikin masana'antar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.