Yayin da ake bukin ranar masu bukata ta musamman a duniya , masu bukata ta musamman a Najeriya sun ce mutumtawa da aiwatar da dokar kula da hakkokin su da gwamnatin Najeriya ta sanyawa hannu tun shekarar 2019, ne kadai kan iya magance matsalolin da suke fuskanta a rayuwa.
Tuggar ya kara da cewa har yanzu suna ci gaba da tattaunawa da hukukomin sojin na Nijar yana mai jaddada cewa kofofin ECOWAS a bude suke a ko da yaushe idan sojojin suna so a tattauna.
Ofishin raya kasashe na kasar Burtaniya ta bullo da sabon Shirin bunkasa harkokin noma da cinikayyar amfanin gona, domin tallafawa kananan manoma a wasu jihohin Najeriya, cikin har da jihar Jigawa.
NAHCON ta ce duk kamfani sai ya gabatar da shaidar mallakar Naira miliyan 30 a ajiye a banki da kuma ba da ajiyar Naira miliyan 25 don kare muradun alhazai idan an saba musu ka'ida.
An rantsar da dan majalisa mai wakiltar Kokona ta Gabas a Majalisar Dokokin jihar Nasarawa, Danladi Jatau na jami'iyyar APC a matsayin sabon Shugaban Majalisar Dokokin jihar.
Wani jirgin yakin rundunar sojojin Najeriya ya yi hatsari da safiyar yau Jumma'a a birnin Fatakwal.
Wasu daga cikin yan Majalisu sun koka da cewa yaudarar su aka yi, domin babu komi a daftarin sai fanko, sai dai wasu na ganin akwai abin dabawa.
A wani yunkuri na sauya fasalin makamashi mai tsafta a duniya da kuma magance matsalar sauyin yanayi, Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya halarci taron COP28 na yanayi a Dubai na wannan shekara.
Arangama tsakanin jami’an banga da 'yan bindiga ta haifar da asarar rayuka sama da 70 a garin Tiggi da ke karamar hukumar Bali a jihar Taraba.
A Najeriya, masharhanta da ke nazari a fagen siyasar kasa da kasa da kuma harkokin diplomasiyya na fashin baki akan koken da kungiyoyi ko jam’iyyun siyasa na kasar ke yi wadanda ke mayar da hannun agogo baya ga ci gaban kasa da nufin neman dauki.
Kamfanin tsare-tsare da bincika na Duke tare da hadin gwiwar Gidauniyar tattalin arziki na Musulunci a Africa sun gudanar da taron na musamman don tattauna hanyar za’a kawo sabbin dabarun duba marasa lafiya a matakin farko tare da basu magani cikin sauki ta hanyar amfani da fasahar zamani.
Dubban matasan da suka mamaye babban titin da ke unguwannin Kurna da Rijiyar Lemo, sun hana masu shiga birnin Kano domin kasuwanci da sauran al’amuran yau da kullum.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.