Daga gobe (Alhamis), ‘'yan Najeriya masu son yin bulaguro za su iya shiga motocin bas na gwamnati a bisa rangwamen kashi 50% na farashin da ake biya a halin yanzu da kuma na jiragen kasa kyauta.” Inji Alake
A ranar Litinin da ta gabata ne Hukumar Kula da Hada-Hadar Kudi ta Amurka (SEC) ta gurfanar da dan kasuwan nan na Najeriya Dozy Mmobuosi da wasu kamfanoni uku wanda shi ne shugabansu, inda ake zargin su da damfarar masu zuba jari.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya rantsar da tsohon Gwamnan Jihar Filato kuma Tsohon Ministan Kwadago da Samar da Aiyukan yi, Barista Simon Bako Lalong, a matsayin Sanata mai wakiltan Filato ta Kudu a Majalisar Dattawa.
Wasu mata ‘yan jarida a arewacin Najeriya sun kaddamar da wani zaure da zai zama na hadin kai don karfafawa mata gwiwa domin yin aikin da samun nasarar gogaiya da sauran ‘yan jarida na kasa.
Yayin da wasu jihohi a Najeriya musamman na arewa ke fuskantar kalubale a bangarori daba daban, hukumomi na duniya na ci gaba da kai dauki domin taimakawa jihohin a sassa daban daban na rayuwa.
Hankali ya koma kotun kolin Najeriya a jajiberin sauraron daukaka karar gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, kan kalubalantar hukuncin kotun daukaka kara da ya soke zaben sa tare da bai wa abokin hamayyar sa Nasiru Yusuf Gawuna nasara.
Biyo bayan nasara da ya samu a kotun daukaka kara, Ministan Kwadagon Najeriya, Simon Lalong, ya yi murabus daga mukaminsa na minista inda ya tsallaka zuwa majalisar dattawa.
‘’Akwai kayyayaki na yaki sosai kuma muna bada tabbaci ce wa za’a ga sakamako mai kyau. Kuma za’a rika tunkararsu duk inda su ke, duk dajin da suke a kai musu farmaki’’, in ji Matawalle.
Babbar Kotun Tarayya da ke birnin tarayya, Abuja ta haramta wa tsohuwar Ministar Mata da Walwalar Al’umma, Pauline Tallen sake rike wani mukamin gwamnati.
Kwamitin Kudi a Majalisar Dokokin Kasa ya yi kira ga hukumomi da ma'aikatun gwamnati masu samar da kudaden shiga su yi kokarin wuce abinda aka kawo a kundin kasafin kudin badi.
Gwamnan jihar Umar Muhammad Bago, ya bayar da wannan umurni ne a wani jawabi da ya gabatar a lokacin kaddamar da wani aikin noman shinkafa a jihar a ranar Lahadi.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi nasarar kawo karshen fitinar da ta kaure a jihar Rivers tsakanin gwamnan Mista Fabura da magoya bayan tsohon maigidansa tsohon gwamna Nyelson Wike, wanda kuma shi ne ministan babban birnin tarayya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.