Wasu ‘yan bindiga sun yi wa ayarin motocin kwanton bauna a kudancin Najeriya, inda suka kashe sojoji hudu da wasu farar hula biyu tare da yin garkuwa da wasu ma’aikatan kasar Koriya biyu, kamar yadda ‘yan sanda suka bayyana a yau Laraba.
Gwamnatin tarayyar Najeriya, ta hannun ma’aikatar ma’adinai ta tarayya, cikin wani gaggarumin yunkuri don bunkasa tattalin arziki a Najeriya, za ta yi hadin gwiwa da babban bankin duniya don samun tallafi wajen bunkasawa da karfafa tattalin arziki na ma’adinai a Najeriya.
Hukumar Alhazan Najeriya NAHCON ta kaddamar da kwamitin tantance kamfanonin jirgin saman fasinja da na dakon kaya don aikin hajjin 2024.
Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta yi Allah wadai da gazawar gwamnatin tarrayya na ci gaba da biyan kudin tallafi ga ma'aikatan gwamnati na Naira 35,000 da aka fara a watan Satumban wannan shekara, domin rage wahalhalu da ake samu sanadiyar cire tallafin man fetur.
Jami'ar tarayya dake Jos a jihar Filato ta kaddamar da katafaren sashe da zai kula da cututtukan koda, mafitsara, mahaifa da sauran cututtuka marasa yaduwa.
Kungiyar kare yancin 'yan kasa da kuma kididdigar ayyuka ta SERAP, ta umarci babban kamfanin albarkatun man-fetur na NNPCL da ya bayyanawa 'yan kasar adadin gangar danyen man da suke haka a duk rana.
Shahararren dan wasan Nigeriya, Victor Osimhen ya zama dan wasa daga nahiyar Afirka na farko da ya lashe kyautar gwarzon dan wasan da yafi kowa zura kwallo a raga a gasar Siriya A ta kasar Italy.
A yayin ziyarar shugaba Bola Tinubu zuwa jihar Borno, ya kaddamar da wasu motocin sufuri da gwamnatin Farfesa Baba Gana Umara Zulum ta sayo a kwanan nan domin sauwaka wa al’ummar jihar zirga-zirga.
Kwararriyar 'yar jarida kuma tsohuwar ma’aikaciyar gidan talabijin na NTA, Aisha Bello ta rasu ranar Lahadi sai dai ba a bayyana sanadin mutuwar ta ba.
Dukkan ‘yan majalisar dattawa 109 na Najeriya sun ce sun sadaukar da albashin su na wannan watan Disamba gaba daya ga iyalan wadanda su ka rasu sanadiyyar harin jirgin saman soji a garin Tudun Biri na jihar Kaduna.
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka, ECOWAS, ta kafa kwamitin mutum uku domin tattaunawa da gwamnatin mulkin sojan Nijar kan batun maida gwamnatin Nijar kan tsarin dimokuradiyya da kuma yin la'akari da sassauta takunkumi, a cewar sanarwar bayan taron kungiyar na duk shekara.
Katafariyar matatar mai da hamshakin attajirin nan Aliko Dangote ya gina a Najeriya ta samu gangunan danyen man fetur na farko, wata gagarumar cigaba na aiki da ya sha fama da jinkiri da nufin biyan bukatun man kasar gaba daya, a cewar sanarwar kamfanin yau Asabar
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.