Rashin zaman lafiya na ci gaba da wanzuwa a wasu yankunan arewacin Najeriya, inda ‘yan bindiga ke garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa tare da sakawa wasu al’umomi haraji na miliyoyin Naira.
Rundunar sojojin Najeriya ta kammala wani atisayen makwanni biyu da ta yi wa lakabi da “Operation Mugun Bugu” wanda shine na biyu a wannan shekara ta 2023.
Jihohin yankin na arewa maso gabashin Najeriya, musamman jihar Borno, sun kwashe sama da shekara goma suna fama da matsalar mayakan Boko Haram.
Dukkanin 'yan majalisar da kotun ta soke zaben nasu 'yan jam'iyyar PDP ne, abin da ke nufin jam'iyyar ta rasa rinjayen da take da shi a mjalisar dokokin.
Hukuncin na zuwa ne yayin da ake ta ce-ce-ku-ce kan yadda kotunan daukaka kara a Najeriya ke rushe zabukan gwamnoni galibi na jam'iyyun adawa.
Ministan kuɗin Najeriya ya bayyana cewa Najeriya ta samu ƙarin kuɗin shiga cikin wata huɗu bayan sauye-sauye da kuma cire tallafin man fetur da shugaba Tinubu yayi, sai dai 'yan Najeriya na ganin ƙarin kuɗin shigar ba wani tasiri zai yi a ƙasar ba, idan har talakawan ƙasar basu gani a ƙasa ba.
Ziyarar tsohon shugaban dai ta janyo hasashe dabam daban daga 'yan Najeriya, game da tasirinta a irin wannan lokaci da kuma makomar siyasar kasar baki daya.
Yayin da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ja kunnen masu yunkurin tada fitina a jihar, kwarraru da ke sharhi kan harkokin tsaro sun ankarar da al’umma game da wasu muhimman al’amura da suka shafi shiga cikin harkokin tarzoma.
Sai dai fadar shugaban kasar ta Najeriya ta ce Babachir yana wadannan kalaman ne saboda har yanzu yana fama da takaicin nasarar da Tinubu ya samu a zaben da aka yi.
Wadansu 'yan aware masu amfani da harshen Ingilishi dauke da makamai sun kai hari wani kauye a kasar Kamaru da yammacin ranar Laraba, inda mutane da dama suka rasa rayukansu.
Kotun daukaka kararrakin zabe dake zama a Abuja ta warware sakar da kotun sauraren kararrakin zabe a jahar Nasarawa tayi, inda ta ayyana gwamna mai ci, Abdullahi Sule a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jahar.
Hukumar alhazan Najeriya NAHCON ta nanata umurnin ajiye Naira miliyan 4.5 daga duk mai niyyar gudanar da aikin Hajjin 2024 gabanin karshen watan gobe.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.