Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya bayyana alhininsa game da rasuwar babban ma’aikacin yada labarai, Kabiru Usman Fagge, wanda ya rasu ranar Juma’a a kasar Amurka.
Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa ta bayar da gudunmuwar kudi Naira miliyan 180 ga wadanda harin bam din ya rutsa da su a Tudun Biri, karamar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.
Tsohon Ma'aikacin Sashen Hausa Alhaji, Kabiru Usman Fagge ya rasu a nan Amurka sakamakon rashin lafiya.
Dokta Chukwuemeka Ezeife, wanda jigo ne a kungiyar kabilar Igbo ta Ohaneze Ndigbo, ya rasu ne a babban asibitin Tarayya da ke Abuja a sakamakon rashin lafiya.
Hukumar yaki da sha ko tu'ammuli da miyagun kwayoyi a Najeriya ta hada hannu da sauran jami'an tsaro domin kara tsaftace al'umma daga illolin tu'ammuli da miyagun kwayoyi, yayin da shekara ta 2023 ke bankwana, bukukuwan Kirsimati da sabuwar shekara ke kara matsowa, .
Kwanaki 16 cir kafin a cika wa’adin da kamfanin man fetur na Najeriya wato NNPCL ya sanya na fara aikin matatar man fetur na Fatakwal, masu ruwa da tsaki a fannin albarkatun man fetur sun nuna shakku ga yiyuwar hakan ganin cewa ba’a ma fara aikin gwaji a matatar da ake sake ginawa din ba.
Mai ba shugaban Najeriya Bola Tinubu shawara kan al’amurran siyasa, Ibrahim Kabir Masari ya ce ba wani dalilin da zai sa shugaban kasar ya yi katsalandan ga lamuran shari'a wanda bangare ne mai cin gashin kan shi.
Tun farko dai ‘yan kasuwar ne suka shigar da gwamnatin Kanon a gaban babbar kotun tarayya da ke Kano, suna kalubalantar matakin gwamna Abba Kabiru Yusuf na rusa musu shaguna, lamarin da suka ce ya jefa rayuwar su da ta iyalan su cikin damuwa.
Majalisar Dinkin Duniya ta kebe kwanaki goma sha shida don yin gangamin yaki da cin zarafi da ya jibanci jinsi, walau mata ko maza a fadin duniya.
Rundunar ‘yan sanda jihar Kano a Najeriya ta gargadi masu sha’awar tada fitina a cikin al’uma su sauya tunani, a dai-dai lokacin da tace ta dukufa wajen bankado wadanda keda hannu wajen cinna wuta a sakatariyar karamar hukumar Gwale ta cikin birnin Kano.
Bankin Duniya ya ce bai kamata Najeriya tana sayar da litar man-fetur a farashin Naira 650 ba, duba da yadda musayar kudaden kasashen ketare suke a yanzu.
Gwamantin Najeriya tasha alwashin cigaba da nemo wasu hanyoyin samun kudaden shiga domin bunkasa tattalin arzikin kasar, maimakon dogaro da man fetur.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.