Shugaban Kungiyar Kwadago ta TUC, Festus Isifo ne ya ayyana shiga yajin aikin a yayin wani taron manema labarai daya gudanar tare da shugabannin kungiyar kwadago ta NLC a Abuja a yau Juma'a.
Sanarwar mai dauke da sa hannun shugaban kamfanin na riko, Victor Ojelabi, ta gargadi kwastomominsa da kodai su biya kudin wutar da suka sha ko kuma ya yanke musu ita.
Da yake sanar da karin girman da aka yiwa jami’in a wani kwarya-kwaryan bikin da Francis Igonoh ya mika shaidar kyautar daya lashe ga Shugaban Hukumar ta NDLEA, Buba Marwa ya yaba mishi saboda sanya hukumar dama Najeriya alfahari a idon duniya.
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana a ranar Juma’a cewa ‘yan aware a yankin kudu maso gabas sun kashe sojoji biyar a wani hari da suka kai a wani shingen binciken ababan hawa.
Najeriya ta samu lamunin dala miliyan 500 da bankin duniya ya baiwa bangarenta na wutar lantarki domin bunkasa rarraba wutar ta lantarki.
Hukumar Kula da ‘Yan Najeriya Mazauna Ketare (NIDCOM) ce ta bayyana hakan a cikin sanarwar data fitar a jiya Laraba.
An kama wani shugaban ‘yan fashi da makami a Najeriya da ake nema ruwa a jallo da yin garkuwa da jama’a tare da mutanensa 65 a kudancin Nijar, kamar yadda hukumomin yankin suka sanar.
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya bayyana cewar ‘yan bindigar sun mamaye kasuwar ta “Maro Junction” ne da misalin karfe 4 da rabi na yammacin jiya Laraba, tare da bude wuta akan mutanen dake cikin kasuwar, inda suka rika harbin kan mai uwa da wabi.
Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da layin dogo na Abuja a hukumance, wanda ke nuna wani gagarumin ci gaba a harkar sufurin Najeriya, musamman a babban birnin na kasar.
A hukuncin daya zartar, Mai Shari'a Ekwo ya sallami Bodejo ne bayan da lauyar dake kare ofishin antoni janar din, Aderonke Imana, ta gabatar da bukatar tare d neman janye tuhume-tuhume 3 da suka gabatar.
Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya ce akwai matakan da ya kamata a dauka kafin gwamnatin Hadaddiyar Daular Larabawa ta koma baiwa ‘yan Najeriya takardar izinin shiga kasar.
Alkalin Alkalan Najeriya, Mai Shari’a Olukayode Ariwoola yayi sammacin Babban Joji a Babbar Kotun Tarayya, Justice John Tsoho da takwararsa ta Babbar Kotun Jihar Kano, Mai Shari’a Dije Aboki akan bada umarni masu cin karo da juna game da masarautar Kano, abinda ya haifar da rudani a jihar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.