A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar, Festus Osifo, a ranar Laraba, yayi allawadai da umurnin na babban bankin Najeriyar ga bankuna a fadin kasar su caza kashi 0.5 cikin 100 a matsayin harajin intanet akan duk wata hada-hadar kudi.
A cewar sanarwar daya wallafa a shafinsa na x, gwamnan yace tsarin zai saukaka tsadar zirga-zirga a cikin birni tare da kawo sauki ga masu amfani da ababen hawan haya a harkokin sufurinsu na yau da kullum.
Babban Bankin Najeriya (CBN) ya fitar da sunayen bankunan ajiya masu lasisi dake gudanar da harkokinsu a kasar.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar ta yanke shawarar gudanar da bincike akan yadda wani babban jami’in kamfanin Binance, Nadeem Anjarwalla, ya arce daga hannun jami’an tsaron Ofishin Mashawarcin Shugaban Kasa Akan Harkokin Tsaro a watan Maris din daya gabata.
Ƙungiyar kare ‘yancin ‘yan ƙasa da Bibiyar Ayyuka ta SERAP ta maka Gwamnonin jihohin 36 na Najeriya da Ministan Abuja babbar kotu a jihar Legas bisa zarginsu da gazawa wajen ƙididdigar ayyukan da suka yi da kudaden lamuni da suka karba da ya kai har dalar Amurka biliyan 4.6 da kuma Naira tiriliyan 5.9.
'Yan Najeriya daga sassan kasar daban-daban ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyinsu da nuna shakku da rashin fahimtar yadda tsarin yake, jim kadan bayan fitowar sanarwar bankin CBN wanda za’a fara aiwatarwa nan da makwanni biyu daga ranar da sakon ya fito.
Wasu matakai da gwamnatin Najeriya ke dauka a baya bayan nan zasu kara kuntata wa talakawa, musamman a yanayin da ake ciki na matsin tattalin arziki, a cewar shugaban kungiyar CISLAC.
Batun rage farashin wutar lantarki a Najeriya dai na ci gaba da jawo muhawara mai karfi ne tun bayan fito da sanarwa da kamfanin rarraba wutan lantarki na Legas wato Ikeja Electric ya yi a ranar Litinin.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da CBN din ya fitar wacce aka rabawa ilahirin bankunan kasuwanci dana bunkasa cinikayya da marasa ta’ammali da kudin ruwa dana biyan kudin ayyuka dana tafi da gidanka.
Hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya ta umarci kamfanin samar da wutar lantarki da ya rage yawan wutar da ake ba abokan hulda a kasashen ketare domin bunkasa samar da wutar lantarki a cikin gida.
Wasu daga cikin tsoffin kwamandojin kungiyar Jama'atu Ahlussunnah lil'da'wati wal jihad da aka fi sani da Boko Haram sun bayyana nadamar irin ta'addancin da suka tafka a matsayinsu na mayakan kungiyar a baya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.