Dillalan mai a Najeriya sun dora alhakin karancin fetur na baya-bayan nan akan tsarin da babban kamfanin man fetur na kasar, NNPCL, ke bi wajen samar musu da shi.
Tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya ya bayyana cewar babu wata kotun jiha a Najeriya da zata iya sauraron shari’ar da ake yi masa kan zargin cin amanar mukami kasancewar hakan zai iya bijiro da batun dacewar hakan bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulki dana shari’a.
‘Yan Najeriya na ci gaba da kokawa game da yadda karancin man fetur da kuma tsadarsa ta mamaye arewacin kasar, bisa yadda al’umma ke shan wahalar samun wannan makamashi da rayuwa ta dogara da shi. Yanzu haka farashinsa ya yi tashin gwauron zabi ya wuce farashin gwamnati.
A shekarar da ta gabata jim kadan bayan da aka rantsar da shi, Tinubu ya cire tallafin mai da gwamnati ke biya wanda ke saukaka farashin mai ga al’umar kasar .
Najeriya ta samu jarin dalar Amurka miliyan 600 na samar da kayayyakin aiki a tashar jiragen ruwa daga kamfanin jigilar kayayyaki na kasar Denmark A.P. Moller-Maersk MAERSKb.CO, kamar yadda fadar shugaban kasar ta fitar ranar Lahadi.
Akalla jami'an rundunar sa-kai ta Civilian JTF ashirin da uku aka kashe a Najeriya a ranar Asabar a wasu hare-hare biyu da mayaka da ‘yan bindiga masu satar mutane suka kai a arewacin kasar.
Fubara ya bayyana hakan ne yayin ziyarar gane wa idonsa da ya kai East-West Road da lamarin ya faru a daren Juma’a inda wata tankar mai ta kama da wuta ta halaka mutane tare da barnata dukiyoyi da dama.
Jim kadan bayan kamalla wani babban taro na musamman a kan yaki da ayyukan ta’adanci a nahiyar Afrika, kasashen nahiyar baki daya sun ce sun shirya tsaf don fitar da sabbin dabarun bai daya na yaki da matsalolin tsaro a matakin shiyya, tare da goyon bayan wasu kungiyoyin kasashen Turai kamar EU.
Bayanai sun yi nuni da cewa bayan da tankar ta kama da wuta, ta shafi motoci akalla goma da ke jerin cunkoson ababen hawa a birnin na Fatakwal.
sanarwar da mai magana da yawun kamfanin, Olufemi Soneye ya fitar tace, an warware matsalar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.