'Yan Najeriya daga sassan kasar daban-daban ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyinsu da nuna shakku da rashin fahimtar yadda tsarin yake, jim kadan bayan fitowar sanarwar bankin CBN wanda za’a fara aiwatarwa nan da makwanni biyu daga ranar da sakon ya fito.
Wasu matakai da gwamnatin Najeriya ke dauka a baya bayan nan zasu kara kuntata wa talakawa, musamman a yanayin da ake ciki na matsin tattalin arziki, a cewar shugaban kungiyar CISLAC.
Batun rage farashin wutar lantarki a Najeriya dai na ci gaba da jawo muhawara mai karfi ne tun bayan fito da sanarwa da kamfanin rarraba wutan lantarki na Legas wato Ikeja Electric ya yi a ranar Litinin.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da CBN din ya fitar wacce aka rabawa ilahirin bankunan kasuwanci dana bunkasa cinikayya da marasa ta’ammali da kudin ruwa dana biyan kudin ayyuka dana tafi da gidanka.
Hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya ta umarci kamfanin samar da wutar lantarki da ya rage yawan wutar da ake ba abokan hulda a kasashen ketare domin bunkasa samar da wutar lantarki a cikin gida.
Wasu daga cikin tsoffin kwamandojin kungiyar Jama'atu Ahlussunnah lil'da'wati wal jihad da aka fi sani da Boko Haram sun bayyana nadamar irin ta'addancin da suka tafka a matsayinsu na mayakan kungiyar a baya.
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, Mansir Hassan, ne ya tabbatar da afkuwar lamarin, inda yace an kama daya daga cikin maharan.
A kokarinsa na maida birnin Kano zuwa katafariyar alkarya, tare da rage mata cunkoson ababen hawa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora harsashin ginin gadar sama mai hawa 3 da zata lakume Naira biliyan 15 a Kofar Dan Agundi.
Hakan na nufin ragin kaso 8.1 cikin 100 akan yadda kudin lantarkin ya kasance a baya kamar yadda hukumar ta NERC ta umarta. Kuma umarnin na NERC ya fara aiki ne tun daga yau.
Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya tashi daga Abuja zuwa birnin Dallas na kasar Amurka, domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a taron kasuwanci na Amurka da Afirka na 2024 wanda kungiyar kamfanoni kan Afirka ta shirya.
Gagarumar ambaliyar ruwa da ta auku a kudancin jihar Rio Grande do Sul a kasar Brazil ta kashe mutane akalla 60 yayin da wasu 101 suka bace, kamar yadda alkaluman hukumomin yankin suka bayyana a ranar Lahadi.
Al’amarin ya faru ne a ranar 1 ga watan nan na Mayu kamar yadda rahotanni suka nuna amma har ya zuwa ranar Lahadi ba a ji duriyarsu ba.
Domin Kari
No media source currently available