Wasu daga cikin tsoffin kwamandojin kungiyar Jama'atu Ahlussunnah lil'da'wati wal jihad da aka fi sani da Boko Haram sun bayyana nadamar irin ta'addancin da suka tafka a matsayinsu na mayakan kungiyar a baya.
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, Mansir Hassan, ne ya tabbatar da afkuwar lamarin, inda yace an kama daya daga cikin maharan.
A kokarinsa na maida birnin Kano zuwa katafariyar alkarya, tare da rage mata cunkoson ababen hawa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora harsashin ginin gadar sama mai hawa 3 da zata lakume Naira biliyan 15 a Kofar Dan Agundi.
Hakan na nufin ragin kaso 8.1 cikin 100 akan yadda kudin lantarkin ya kasance a baya kamar yadda hukumar ta NERC ta umarta. Kuma umarnin na NERC ya fara aiki ne tun daga yau.
Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya tashi daga Abuja zuwa birnin Dallas na kasar Amurka, domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a taron kasuwanci na Amurka da Afirka na 2024 wanda kungiyar kamfanoni kan Afirka ta shirya.
Gagarumar ambaliyar ruwa da ta auku a kudancin jihar Rio Grande do Sul a kasar Brazil ta kashe mutane akalla 60 yayin da wasu 101 suka bace, kamar yadda alkaluman hukumomin yankin suka bayyana a ranar Lahadi.
Al’amarin ya faru ne a ranar 1 ga watan nan na Mayu kamar yadda rahotanni suka nuna amma har ya zuwa ranar Lahadi ba a ji duriyarsu ba.
Wasu ‘yan bindiga daga kungiyoyin miyagu sun kashe mutane 25 a lokacin da suka kai farmaki a wasu kauyuka hudu a yankin arewa maso yammacin Najeriya, a matsayin ramuwar gayya saboda farmakin da sojoji suka kai maboyarsu, a cewar wani jami’in tsaro a yankin.
Gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN, Olayemi Cardoso ya ce kayayyakin abincin da gwamnati take saya don rabawa mabukata na daga cikin dalilan da suke kara hauhawar farashin kayayyaki a kasar.
‘Yan bindiga sun hallaka akalla ‘yan sintiri 8 da wasu mutane 2 a kauyukan Kakangi da Unguwan Matinja dake karamar hukumar Birnin Gwarin jihar Kaduna.
Harin na ranar 3 ga watan Disambar 2023, na daya daga cikin kurakurai mafiya muni a hare-haren da jiragen sojin saman kasar suka kai kan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.