Hukumar Kula da ‘Yan Najeriya Mazauna Ketare (NIDCOM) ce ta bayyana hakan a cikin sanarwar data fitar a jiya Laraba.
An kama wani shugaban ‘yan fashi da makami a Najeriya da ake nema ruwa a jallo da yin garkuwa da jama’a tare da mutanensa 65 a kudancin Nijar, kamar yadda hukumomin yankin suka sanar.
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya bayyana cewar ‘yan bindigar sun mamaye kasuwar ta “Maro Junction” ne da misalin karfe 4 da rabi na yammacin jiya Laraba, tare da bude wuta akan mutanen dake cikin kasuwar, inda suka rika harbin kan mai uwa da wabi.
Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da layin dogo na Abuja a hukumance, wanda ke nuna wani gagarumin ci gaba a harkar sufurin Najeriya, musamman a babban birnin na kasar.
A hukuncin daya zartar, Mai Shari'a Ekwo ya sallami Bodejo ne bayan da lauyar dake kare ofishin antoni janar din, Aderonke Imana, ta gabatar da bukatar tare d neman janye tuhume-tuhume 3 da suka gabatar.
Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya ce akwai matakan da ya kamata a dauka kafin gwamnatin Hadaddiyar Daular Larabawa ta koma baiwa ‘yan Najeriya takardar izinin shiga kasar.
Alkalin Alkalan Najeriya, Mai Shari’a Olukayode Ariwoola yayi sammacin Babban Joji a Babbar Kotun Tarayya, Justice John Tsoho da takwararsa ta Babbar Kotun Jihar Kano, Mai Shari’a Dije Aboki akan bada umarni masu cin karo da juna game da masarautar Kano, abinda ya haifar da rudani a jihar.
Nan bada jimawa ba Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai gabatar da karamin kasafin kudin bana ga Majalisar Dokokin Kasar.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya tabbatar da hakan yayin zaman hadakar majalisar a yau Laraba.
Sai dai wasu 'yan majalisar sun nuna takaicinsu kan wannan mataki da majalisar ta dauka.
Malaman addini da wani ‘dan majalisar dokokin jiha sun dakatar da shirinsu na aurar da mata da ‘yan mata 100 a yankin Arewacin Najeriya bayan da lamarin ya haifar da bacin rai.
Domin Kari
No media source currently available