Gwamnatin jihar Kaduna ta fito da wani tsari na hada makarantu 359 wuri daya saboda karuwan ayyukan ‘yan fashin daji lamarin da yasa aka samu yawan sace mutane da yin garkuwa dasu a jihar.
An gurfanar da Hadi Sirika ne a gaban Mai Shari’a Sylvanus Oriji na babbar kotun tarayya da ke zamanta a birnin Abuja tare da diyarsa, Fatima, da surkinsa, Jalal Sule Hamma, da wani kamfani mai suna Al Buraq Global Investment Limited.
Hakan wani martani ne ga bukatar gaggawa da dan majalisa Kingsley Chinda ya gabatar yana bukatar a dakatar tare da yiwa shirin aiwatar dokar harajin tsaron intanet din kwaskwarima.
Kwararru da masana daga Afirka ta yamma sun gudanar da wani nazarin sabbin dabarun tunkarar aiyukan ta'addanci da ke kara ta'azzara a yankin a halin yanzu.
A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar, Festus Osifo, a ranar Laraba, yayi allawadai da umurnin na babban bankin Najeriyar ga bankuna a fadin kasar su caza kashi 0.5 cikin 100 a matsayin harajin intanet akan duk wata hada-hadar kudi.
A cewar sanarwar daya wallafa a shafinsa na x, gwamnan yace tsarin zai saukaka tsadar zirga-zirga a cikin birni tare da kawo sauki ga masu amfani da ababen hawan haya a harkokin sufurinsu na yau da kullum.
Babban Bankin Najeriya (CBN) ya fitar da sunayen bankunan ajiya masu lasisi dake gudanar da harkokinsu a kasar.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar ta yanke shawarar gudanar da bincike akan yadda wani babban jami’in kamfanin Binance, Nadeem Anjarwalla, ya arce daga hannun jami’an tsaron Ofishin Mashawarcin Shugaban Kasa Akan Harkokin Tsaro a watan Maris din daya gabata.
Ƙungiyar kare ‘yancin ‘yan ƙasa da Bibiyar Ayyuka ta SERAP ta maka Gwamnonin jihohin 36 na Najeriya da Ministan Abuja babbar kotu a jihar Legas bisa zarginsu da gazawa wajen ƙididdigar ayyukan da suka yi da kudaden lamuni da suka karba da ya kai har dalar Amurka biliyan 4.6 da kuma Naira tiriliyan 5.9.
'Yan Najeriya daga sassan kasar daban-daban ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyinsu da nuna shakku da rashin fahimtar yadda tsarin yake, jim kadan bayan fitowar sanarwar bankin CBN wanda za’a fara aiwatarwa nan da makwanni biyu daga ranar da sakon ya fito.
Wasu matakai da gwamnatin Najeriya ke dauka a baya bayan nan zasu kara kuntata wa talakawa, musamman a yanayin da ake ciki na matsin tattalin arziki, a cewar shugaban kungiyar CISLAC.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.