Jami’in Majalisar Dinkin Duniyar ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da shirin Yaki da Karancin Abinci na bana.
A shekara ta 2022 ne shugaban bankin raya musulinci wato IDB, Dr Muhammad Al-Jasser ya kaddamar da shirin bankin na raya noma da kiwo a jihar Kano da nufin samar da abinci da dakile rikici tsakanin manoma da makiyaya
Mataimakin kwamandan hukumar Hisbah Dr. Mujahidin Aminuddin Abubakar ya yi kira ga iyaye da su sa ido sosai kan harkokin ‘ya’yansu.
A watan daya gabata, IPMAN tayi barazanar durkusar da harkar samarda man fetur a Najeriya, akan rashin biyan bashin Naira biliyan 200 ta kudaden dakon man.
Lauyan Hukumar EFCC, mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati, Oluwaleke Atolagbe, ya shaidawa alkalin kotun, Mai Shari’a Suleiman Belgore, cewar ba’a mikawa tsohon ministan da kaninsa sammacin dake kunshe da tuhumar a cikinsa ba.
Wasu ‘yan bindiga da suka yi garkuwa da mutane 105 a yankin Arewa maso yammacin Najeriya a makon da ya gabata, ba kudin fansa su ke so ba, tattaunawa su ke so da gwamnatin jihar Zamfara, kamar yadda wasu iyalai biyar suka shaida bayan da ‘yan bindigar suka tuntube su a ranar Litinin.
‘Yan Najeriya daga shiyoyin kasar kama daga Kano, Filato, Bauchi, Kaduna, Neja da dai sauransu sun ce lallai kungiyoyin sun rufe ofisoshin DisCos amma ba su ga wani tasiri da zanga-zangar ya yi a kasar ba.
Shugaban Hukumar bada agajin gaggawa na jihar Yobe wato YOSEMA, Dakta Mohammed Goje ne ya bayyana hakan a yayın hira ta musamman ga Muryar Amurka.
Wata majiyar soji ta bayyana cewar an samu nasarar kubutar da mutanen ne sakamakon samun wani kiran gaggawa a ranar 11 ga watan Mayun da muke ciki, da misalin karfe 12 rana.
Shigar da karar ya biyo bayan faifan bidiyon daya karade shafukan sada zumunda a ‘yan makonnin da suka gabata inda aka wasu dalibai suna cin zalin Namitra Bwala.
Matakin ma’aikatan na zuwa ne biyo bayan umarnin hadin gwiwa da kungiyar kwadago ta Nlc da takwararta ta Tuc suka baiwa mambobinsu a karshen mako na cewa su kargame ofisoshin domin nuna adawa da karin kudin wuta.
A ranar Alhamis wasu ‘yan bindiga suka kutsa jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Osara a jihar Kogi suka kwashi dalibai da dama suka yi cikin daji da su.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.