A ranar Alhamis 23 ga watan Mayu nan ne shugaban kasa Bola Tinubu zai bar Abuja zuwa birnin N’Djamena na Jamhuriyar Chadi domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Idriss Mahamat Deby Itno.
Mai shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya bayar da belin tsohon kwamandan rundunar ‘yan sandan farin kaya DCP Abba Kyari na wucin gadi na tsawon makonni biyu bisa dalilai na alfarma da ya je ya halarcin zaman makokin mahaifiyarsa.
Obasanjo ya bayyana hakan ne yayin wani taro game da yanayin dimokradiya a nahiyar Afirka daya gudana a cibiyar 'Yar’adua dake Abuja a yau Laraba.
Da yake tabbatar da mutuwar DPOn a yau Laraba, kakakin rundunar 'yan sanda jihar Borno, Nahun Kenneth, yace har yanzu rundunar na tattara bayanai akan harin.
A cewar kakakin Hukumar EFCC, Dele Oyewale, an ga Janty Emmanuel tana watsa kudin a wurin taro na G-Connect dake shiyar Tumfure ta jihar Gombe, a ranar Litinin 20 ga watan Mayun da muke ciki.
A cewar Bankin Raya Afirka (AfDB), akalla mutane miliyan 600 a nahiyar Afirka ke fama da rashin wutar lantarki, ciki kuwa harda Najeriya, inda har yanzu mutane miliyan 90 ba sa da wutar lantarki.
Wani yaro mai shekara biyu na daga cikin mutane 12 da rundunar hadin gwiwa ta jami’an tsaro a Najeriya ta ceto daga hannun masu garkuwa da mutane a jihar Kwara a ranar Litinin.
Alhaji Atiku, wadda karo na biyar kenan da ya tsaya takarar shugaban kasar bayan dawowar Najeriya dimokraddiya a shekarar 1999, a zaben da aka gudanar a shekarar 2023, ya ce “insha Allahu” da aka yi masa tambayar ko zai tsaya takara a zaben 2027.
An ceto akalla mutum 22 da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su daga gundumar Dawaki da ke birnin Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya, kamar yadda ‘yan sanda da mazauna yankin suka bayyana a ranar Talata.
Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso ne ya bayyana daukan wannan matakin jim kadan bayan kamalla taron manufofin kudi na yini biyu a yau Talata inda aka kara kudin ruwa da maki 150 kuma a yanzu yake kan kaso 26 da digo 25.
Yayin da take gabatar da kudirin mai matukar mahimmanci ga kasa, majalisar ta bukaci Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo ya gudanar da cikakken bincike akan ma’aikatan dake aiki a tashoshin jiragen saman najeriya.
Kungiyoyi masu faftuka na nuna shakku tare da zargin rundunar 'yan sanda da yin rufa-rufa da batun jami'ar 'yar sanda da aka kama da hannu ga satar kananan yara daga Sakkwato har zuwa Abuja.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.