Da farko dai ‘yan bindigar sun yi awon gaba ne da basarake da matarsa daga fadarsa da ke Fadan-Ninzo a daren Laraba tare da wasu mazauna unguwar.
Da misalin karfe 12 na ran nan ne alkalin kotun mai sharia M.A Liman ya zauna domin sauraron shari'ar.
Sanata Titus Zam mai wakiltar mazabaar Benuwe ta arewa maso yamma, gabatar da hujjar cewa za'a iya shawo kan matsalar rikicin manoma da makiyaya ta hanyar yin dokar da zata haramta kiwo a sake a fadin Najeriya.
Gwamnatin Kano na tuhumar Ganduje da mai dakinsa, Hafsat Umar da wadansu mukarrabansa da zargin aikata laifuffuka 10 masu nasaba da cin hanci da almundahana da karkatar da kudaden al’umma na biliyoyin Naira
Da yake gabatar da rahoton yayin zaman majalisar na ranar laraba, Shugaban Kwamitin, Henry Zacharia, yace ba’a yi amfani da galibin basussukan da gwamnatin El-Rufa’i ta ranto akan bukatun da suka sa aka karbosu ba, a yayin da wasu lokotanma, ba abi ka’idojin karbo bashin ba.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, Muhammad Dalijan ne ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin jami’in da ke kula da sashin yaki da ta’addanci a karkashin ofishin Majalisar Dinkin Duniya kan yaki da miyagun kwayoyi (UNODC).
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya umurci Ministan Kudi na kasar, Wale Edun, da ya gabatar da tsarin da gwamnati za ta bi na aiwatar da sabon adadin albashin ma’aikata mafi karanci.
Masu ba da lamuni a Najeriya sun fara gabatar da tsare-tsaren cika sabbin sharuddan gudanar da hada-hadar kudi da babban bankin kasar ya bullo da su a watan Maris don karfafa hada-hadar kudi.
Jami’an ‘yan sandan shiyar Tudun Wadan Zariya ne suka kama wanda ake zargin, mai suna Hussaini a unguwar Tudun Jukun sakamakon samun sahihan bayanan sirri game da take-takensa.
Al’amarin daya afku da misalin karfe 9 da rabi na safiya ya hada da wata tanka da ake zargin tana dauke ne da iskar gas wacce ta latse wata karamar mota tare da tarwatsewa a yayin da take kokarin shiga shatale-tale.
Ko da yake har yanzu babu cikakken bayanai kan harin, sai dai hukumomin sojin sun tabbatar da hakan a wata sanarwa da suka fitar a ranar Talata.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.