Ruwan sama babu kakkautawa da ake samu a baya-bayan nan ya sabbaba ambaliya a wasu jihohi da birnin tarayya Abuja, al’amarin daya sanya Ministan bukatar gwamnatocin jihohin kasar su tsananta kokarin da suke yi na yashe magudanan ruwa.
An nada alkalan kotunan Kanon guda 2 ne domin su shugabancin kwamitocin bincike akan dawo da dukiya da kadarorin al’umma da aka wawure da kuma binciken tashe-tashen hankulan dake da nasaba da siyasa da batan mutane.
Mijin alkaliyar Musa Gimba ya tabbatar da sakin na ta sai dai yace ana cigaba da yin garkuwa da ‘ya’yanta 3.
Rundunar ‘yan Sandan jihar Delta ta yi kira ga wadanda ake cin zarafin su a gidajen aure, musamman mata su kai kara a ofishin ‘yan Sanda mafi kusa a maimakon yin korafi a dandalin sada zumunta.
Tsohon hafsan mayakan ruwa, Admiral Allison Madueke mai ritaya wanda kuma ya yi gwamna a jihohin Anambra da Imo ya bukaci kotu ta umarci tsohuwar Minister Diezani Allison- Madueke ta daina amfani da sunan shi, ta koma amfani da sunan mahaifinta Agama domin daina bata mashi suna.
Jakadiyar Tarayyar Turai a Najeriya da Kungiyar Raya Kasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), Samuela Isopi, ce ta bayyana hakan a yayin taron bunkasa kasuwanci tsakanin Najeriya da kungiyar kasashen Turai (EU) karo na 9 da ya gudana a Abuja a yau Talata.
‘Yan bindiga sun hallaka wani malami a jami’ar tarayya ta Dutsin-Ma dake jihar Katsina.
Jami’an hukumar bada agajin gaggawan sun dora alhakin faruwar lamarin akan dan kwangilar, saboda bijirewa umarnin da Hukumar Kula da Gine-Gine ta birnin Abuja ta bashi na ya dakatar da aiki.
Masana sun bayyana mata da ke kai harin kunar bakin wake a matsayin makaman ‘yan ta’adda na boye, kasancewa ba a zaton za su iya kai irin wannan harin.
Domin Kari
No media source currently available