An kasha akalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan kunar bakin wake ne suka kai a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.
‘Yan bindiga dauke da muggan makamai sun yi garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawakin siyasar nan Dauda Adamu Kahutu, wanda aka fi sani da Rarara.
Wata mummunar gobarar da ta auku a kasuwar Karu da ke Karamar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa ta yi sanadin janyo asarar dukiya mai yawa.
Wanan mataki da Majalisar ta dauka ya biyo bayan wata wasika ne da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiko wa Majalisar inda ya bukaci a kara wa'adin aiwatar da kasafin kudi na Naira triliyan 21.83 na shekara 2023 wanda gwamnatin Tinubun ya gada daga gwamnatin da ta gabata.
Mataimakin shugaban kasar ne ya jagoranci taron da gwamnonin jihohi da mataimakan gwamnoni da ministoci kafin isowar shugaban kasar.
An ruwaito takardar bayan taron da kungiyar gwamnonin ta fitar na cewa, “gwamnonin sun amince su cigaba da tattaunawa da muhimman masu ruwa da tsaki domin samun matsayar da dukkanin bangarorin zasu amince da ita.”
A yau Alhamis aka bayyana hakan, a yayin da Shugaban Majalisar Dattawan, Godswill Akpabio ya jagoranci zamanta bayan dawowa daga hutu domin cigaba da sabon zango a ayyukan majalisar.
Hukumomin Najeriya sun ayyana dokar ta-baci a kasar tare da kaddamar da matakan dakile yaduwar cutar amai da gudawa da ake kira kwalara, wadda ta hallaka mutane sama da 50.
Da safiyar Laraban nan ne aka wayi gari da samun tashin gobara a matatar man fetur ta Dangote a jihar Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya.
Domin Kari
No media source currently available