Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yau Alhamis yayin taron kolin zaman lafiya da tsaro a shiyar arewa maso yammacin Najeriya daya gudana a jihar Katsina.
Gwamnatin jihar Ogun a Najeriya ta tabbatar da kamuwar mutane 25 da cutar kwalara a kananan hukumomi bakwai na jihar, yayin da mutum daya ya rasa ransa a karamar hukumar Ijebu ta Arewar jihar.
Mataimakin shugaban kasar ya bayyana hakan ne a taron kolin zaman lafiya da tsaro a jihohin arewa maso yammacin Najeriya dake gudana a jihar Katsina da ake yadawa kai tsaye a tashar talabijin ta Channels.
Babban daraktan kungiyar MURIC, Farfesa Ishaq Akintola, ne ya bayyana damuwar a cikin sanarwar daya fitar a yau Litinin, inda yace al'ummar Musulmin Najeriya ba zasu amince da duk wani tunani na tube Sarkin Musulmi ba.
Hukumar hana sha da fataucin kwayoyi a Najeriya tace zata rika binciken wuraren da ake wannan dabi'ar da suka hada da gidaje da otel-otel, kuma duk wurin da aka kama da laifi za'a kwace shi a mallakawa gwamnatin tarayya.
Akalla mutane bakwai ne aka kashe tare da yin garkuwa da 100 a daren Asabar bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari a kauyukan jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Manoma a Najeriya na kokawa akan tashin farashin takin noma inda suke kira ga gwamnatin kasar da ta duba lamarin su, yayin da wasu masana ke cewa dole ne a dauki matakan gaggawa, yayin da damina ke kara shigowa gadan-gadan.
Jami'an tsaro a Najeriya sun sanar da samun nasarar kashe wani kasurgumin dan bindiga mai suna Alhaji Kachalla Ragas, wanda ya shahara wajen kai hare hare da kuma satar mutane domin neman kudin fansa a wasu sassan jihar Kaduna da jihohi makwabta.
Yau shekaru 30 da suka gabata, kwallayen da rashidi yekini da daniel amokachi da emmanuel amunike suka ci sun taimakawa tawagar super eagles yin bajinta a fitowarta ta farko.
Sanarwar da ofishin hukumar mai kula da yankin gabashin Tekun Maditereniyan ya fitar tace, an samu barkewar annobar ne daga ranakun 1 ga watan Janairu zuwa 26 ga watan Mayun daya gabata.
A cewar wani kundin sauya fasalin aikin na Bankin Duniyan, gwamnatin Najeriya ta bukaci a tsawaita wa'adin kawo karshen aikin daga ranar 30 ga watan Yunin da muke ciki, zuwa 31 ga watan Disamban badi.
A cewar rahoton masana a cibiyar Clingendael, kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayin da aka yi ittifakin suna da alaka da al-qaeda suka rika tsallakowa daga yankin arewacin jamhuriyar Benin sun samu mafaka a gandun dajin gwamnati dake Kainji, daya daga cikin mafiya girma a Najeriya.
Domin Kari
No media source currently available