Nan bada jimawa ba Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai gabatar da karamin kasafin kudin bana ga Majalisar Dokokin Kasar.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya tabbatar da hakan yayin zaman hadakar majalisar a yau Laraba.
Sai dai wasu 'yan majalisar sun nuna takaicinsu kan wannan mataki da majalisar ta dauka.
Malaman addini da wani ‘dan majalisar dokokin jiha sun dakatar da shirinsu na aurar da mata da ‘yan mata 100 a yankin Arewacin Najeriya bayan da lamarin ya haifar da bacin rai.
Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar, Abba Morro ne ya fara gabatar da kudirin neman a dawo da dakataccen sanatan a yau Talatar, inda ya bayyana nadama a madadinsa.
Kudirin, wanda cikin hanzari ya tsallake karatu na 1 dana 2 a Alhamis din data gabata, yanzu haka yana dakon sa hannun Shugaba Bola Tinubu domin zama doka.
A sanarwar daya fitar, Akawun Majalisar Tarayyar, Sani Tambuwal, yace Shugaban Kasar zai yiwa 'yan majalisun jawabi ne game da halin da kasa ke ciki tare da kaddamar da dakin karatun majalisar.
Hukumomin sun ce "sun zo ne a kan babura kusan 100 kowannensu dauke da mutane uku."
Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya yi kira ga kawayen kasar da a hada kai domin magance matsalar ‘yan gudun hijira a kasar.
Hafsan Hafsoshin Sojin Najeriya Janar Christopher Musa ya bayyana cewa, al’ummar kasar na da gagarumar gudummuwar da za su iya badawa a yunkurin shawo kan matsalar tsaro da ake fuskanta a kasar.
Gwamnatin jihar Kano ta janye zargin da ta yi wa Nuhu Ribadu, mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro na cewa da hannunsa a rikicin masarautar jihar Kano.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.