Mai Shari'a Yellim Bagoro ne ya bada umarnin a jiya Alhamis 23 ga watan Mayun da muke ciki, sakamakon bukatar da lauyan Hukumar EFCC mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa, Bilkisu Buhari, ta gabatar.
An mayar da Sanusi Muhammadu a matsayin Sarkin Kano bayan ya karbi takardar nadinsa daga Gwamna Abba Yusuf ranar Juma'a.
Mai shari’a Mohammed Liman ne ya mika wannan umarnin ga gwamnatin ta Kano.
Kudirin da daya daga cikin jagororin majalisar, Opeyemi Bamidele, ya gabatar ya samu gagarumin goyan baya daga 'yan majalisar.
Hakan ya biyo bayan wani mataki da Majalisar ta dauka a zaman da ta yi ranar Alhamis, 22 ga watan Mayun da muke ciki.
A ranar Alhamis 23 ga watan Mayu nan ne shugaban kasa Bola Tinubu zai bar Abuja zuwa birnin N’Djamena na Jamhuriyar Chadi domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Idriss Mahamat Deby Itno.
Mai shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya bayar da belin tsohon kwamandan rundunar ‘yan sandan farin kaya DCP Abba Kyari na wucin gadi na tsawon makonni biyu bisa dalilai na alfarma da ya je ya halarcin zaman makokin mahaifiyarsa.
Obasanjo ya bayyana hakan ne yayin wani taro game da yanayin dimokradiya a nahiyar Afirka daya gudana a cibiyar 'Yar’adua dake Abuja a yau Laraba.
Da yake tabbatar da mutuwar DPOn a yau Laraba, kakakin rundunar 'yan sanda jihar Borno, Nahun Kenneth, yace har yanzu rundunar na tattara bayanai akan harin.
A cewar kakakin Hukumar EFCC, Dele Oyewale, an ga Janty Emmanuel tana watsa kudin a wurin taro na G-Connect dake shiyar Tumfure ta jihar Gombe, a ranar Litinin 20 ga watan Mayun da muke ciki.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.